< 2 Sama’ila 21 >

1 Lokacin da Dawuda yake mulki, an yi yunwa shekara uku a jere; saboda haka Dawuda ya nemi nufin Ubangiji. Ubangiji ya ce, “Saboda Shawulu ne da alhakin jinin gidansa; domin ya kashe Gibeyonawa.”
There was a famine in David's time for three years in a row, and David sought the face of Yahweh. So Yahweh said, “This famine is on you because of Saul and his murderous family, because he put the Gibeonites to death.”
2 Sai sarki ya tattara Gibeyonawa ya yi musu magana. (To, Gibeyonawa ba sashen Isra’ilawa ba ne, amma mutanen Amoriyawa ne da suka ragu, waɗanda Isra’ila ta rantse za tă bari da rai, amma Shawulu cikin kishinsa don Isra’ila da Yahuda ya yi ƙoƙari yă hallaka su duka.)
Now the Gibeonites were not from the people of Israel; they were from what remained of the Amorites. The people of Israel had sworn not to kill them, but Saul tried to kill them all anyway in his zeal for the people of Israel and Judah.
3 Dawuda ya ce wa Gibeyonawa, “Me zan yi muku? Yaya zan yi kafara domin ku sa wa masu gādon Ubangiji albarka?”
So King David called together the Gibeonites and said to them, “What should I do for you? How can I make atonement, so that you may bless the people of Yahweh, who inherit his goodness and promises?”
4 Gibeyonawa suka ce, “Ba mu da’yanci mu nemi zinariya ko azurfa daga wurin Shawulu ko gidansa, ba mu kuwa da wani’yanci mu sa a kashe wani a Isra’ila.” Dawuda ya ce, “To, me kuke so in yi muku?”
The Gibeonites responded to him, “It is not a matter of silver or gold between us and Saul or his family. In the same way it is not for us to put to death any man in Israel.” David replied, “What are you saying that I should do for you?”
5 Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya hallaka mu ya kuma yi mana makirci don kada mu kasance tare da Isra’ilawa ko’ina a cikin ƙauyukansu,
They answered the king, “The man who tried to kill us all, who schemed against us, so that we are now destroyed and have no place within the borders of Israel—
6 a ba mu zuriyarsa maza bakwai, mu kashe su, mu kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji a Gibeya na Shawulu wannan zaɓaɓɓen Ubangiji.” Sai sarki ya ce, “Zan ba ku su.”
let seven men from his descendants be handed over to us, and we will hang them before Yahweh in Gibeah of Saul, the one chosen by Yahweh.” So the king said, “I will give them to you.”
7 Sarki ya ware Mefiboshet ɗan Yonatan jikan Shawulu, saboda rantsuwar da take tsakanin Dawuda da Yonatan, ɗan Shawulu a gaban Ubangiji.
But the king spared Mephibosheth son of Jonathan son of Saul, because of Yahweh's oath between them, between David and Jonathan son of Saul.
8 Amma sarki ya ɗauki Armoni da Mefiboshet,’ya’ya biyu maza waɗanda Rizfa’yar Aiya ta haifa wa Shawulu, tare da’ya’ya maza biyar na Merab’yar Shawulu, waɗanda ta haifa wa Adriyel ɗan Barzillai, mutumin Mehola.
But the king took the two sons of Rizpah daughter of Aiah, sons whom she bore to Saul—the two sons were named Armoni and Mephibosheth; and David also took the five sons of Merab daughter of Saul, whom she bore to Adriel son of Barzillai the Meholathite.
9 Ya ba da su ga Gibeyonawa, waɗanda suka kashe su, suka kuma rataye jikunansu a gaban Ubangiji. Dukan bakwai ɗin an kashe su gaba ɗaya; an kashe su a farkon kwanankin girbi, daidai lokacin fara girbin sha’ir.
He handed them over into the hands of the Gibeonites. They hanged them on the mountain before Yahweh, and they died all seven together. They were put to death during the time of harvest, during the first days at the beginning of barley harvest.
10 Rizfa’yar Aiya ta ɗauki tsumma ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutse. Tun daga farkon girbi har ruwa damina ya sauko a kan gawawwakin, ba tă yarda tsuntsayen sama su taɓa su da rana ko mugayen namun jeji da dare ba.
Then Rizpah, the daughter of Aiah, took sackcloth and spread it for herself on the mountain beside the dead bodies, from the beginning of harvest until the rain poured down on them from the sky. She did not allow the birds of the sky to disturb the bodies by day or the wild animals by night.
11 Da aka gaya wa Dawuda abin da Rizfa’yar Aiya ƙwarƙwaran Shawulu ta yi,
It was told to David what Rizpah, the daughter of Aiah, the slave wife of Saul, had done.
12 sai ya je ya kwashe ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga mutanen Yabesh Gileyad (Gama mutanen sun saci gawawwakin Shawulu da Yonatan daga inda Filistiyawa suka kakkafa su a kan itace a filin Bet-Shan, bayan da Filistiyawa suka kashe su a Gilbowa.)
So David went and took the bones of Saul and the bones of Jonathan his son from the men of Jabesh Gilead, who had stolen them from the public square of Beth Shan, where the Philistines had hanged them, after the Philistines had killed Saul in Gilboa.
13 Dawuda ya kawo ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan daga can, a kuma aka tattara dukan ƙasusuwan waɗanda Gibeyonawan suka kashe, suka kuma rataye.
David took away from there the bones of Saul and the bones of Jonathan his son, and they gathered the bones of the seven men who had been hanged, as well.
14 Suka binne ƙasusuwan Shawulu da na ɗansa Yonatan a kabarin Kish, mahaifin Shawulu, a Zela a Benyamin. Suka kuma yi kome da sarki ya umarta. Bayan wannan Allah ya ji addu’arsu a madadin ƙasar.
They buried the bones of Saul and Jonathan his son in the country of Benjamin in Zela, in the tomb of Kish his father. They performed all that the king commanded. After that God answered their prayers for the land.
15 Har yanzu yaƙi ya sāke ɓarke tsakanin Filistiyawa da Isra’ila. Sai Dawuda ya gangara tare da mutanensa don su yaƙi Filistiyawa, gajiya ta kama shi.
Then the Philistines went to war again with Israel. So David went down with his army and fought against the Philistines. David was overcome with battle fatigue.
16 Ishbi-Benob kuwa, wani daga zuriyar Rafa, wanda nauyin kan māshinsa na tagulla ya yi shekel ɗari uku, wanda yake kuma da sabon māshi, ya ce zai kashe Dawuda.
Ishbi-Benob, a descendant of the giants, whose bronze spear weighed three hundred shekels, and who was armed with a new sword, intended to kill David.
17 Amma Abishai ɗan Zeruhiya ya kawo wa Dawuda gudummawa; ya bugi Bafilistin, ya kashe shi. Sa’an nan mutanen Dawuda suka rantse masa suka ce, “Ba za ka ƙara fita tare da mu wurin yaƙi ba, don kada fitilar Isra’ila tă mutu.”
But Abishai son of Zeruiah rescued David, attacked the Philistine, and killed him. Then the men of David swore to him, saying, “You must not go to battle anymore with us, so that you do not put out the lamp of Israel.”
18 Ana nan, sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa, a Gob. A lokacin Sibbekai mutumin Husha ya kashe Saf, wani daga zuriyar Rafa.
It came about after this that there was again a battle with the Philistines at Gob, when Sibbekai the Hushathite killed Saph, who was one of the descendants of the Rephaim.
19 Sai aka sāke yin wani yaƙin da Filistiyawa a Gob, Elhanan ɗan Ya’are-Oregim mutumin Betlehem ya kashe Goliyat mutumin Gat, wanda girmar sandan māshinsa ta yi kama da taɓarya.
It came about again in a battle with the Philistines at Gob, that Elhanan son of Jair the Bethlehemite killed Goliath the Gittite, the staff of whose spear was like a weaver's beam.
20 Har wa yau a wani yaƙin da aka yi a Gat, akwai wani ƙaton mutum mai yatsotsi shida a kowane hannu, da kuma yatsotsi shida a kowane ƙafa, yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi ma daga zuriya Rafa ne.
It came about in another battle at Gath that there was a man of great height who had six fingers on each hand and six toes on each foot, twenty-four in number. He also was descended from the Rephaim.
21 Da ya yi wa Isra’ila reni, sai Yonatan ɗan Shimeya, ɗan’uwa Dawuda, ya kashe shi.
When he taunted Israel, Jonathan son of Shimeah, David's brother, killed him.
22 Waɗannan huɗu zuriyar Rafa ne a Gat, suka kuwa mutu ta hannu Dawuda da mutanensa.
These were descendants of the Rephaim of Gath, and they were killed by the hand of David and by the hand of his soldiers.

< 2 Sama’ila 21 >