< 2 Sama’ila 10 >

1 Ana nan sai sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa Hanun kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Nogen Tid efter døde Ammomiternes Konge, og hans Søn Hanun blev Konge i hans Sted.
2 Dawuda ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan yi wa Hanun ɗan Nahash alheri kamar yadda mahaifinsa ya yi mini.” Saboda haka sai Dawuda ya aiki jakadu su yi masa ta’aziyyar mutuwar mahaifinsa. Sa’ad da mutanen Dawuda suka isa ƙasar Ammonawa,
Da tænkte David: "Jeg vil vise Hanun, Nahasj's Søn, Venlighed, ligesom hans Fader viste mig Venlighed." Og David sendte Folk for at vise ham Deltagelse i Anledning af hans Faders Død. Men da Davids Mænd kom til Ammoniternes Land.
3 sai manyan mutanen Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama mahaifinka ne da ya aiko da jakadu su kawo maka ta’aziyya? Ai, wayo ya yi don yă ga asirin birninmu, yă san ƙarfinmu, yă kuma ci mu da yaƙi.”
sagde Ammoniternes Høvdinger til deres Herre Hanun: "Tror du virkelig, det er for at hædre din Fader, at David sender Bud og viser dig Deltagelse? Mon ikke det er for at udforske og udspejde Byen og ødelægge den, at David sender sine Folk til dig?"
4 Saboda haka Hanun ya kama mutanen Dawuda ya aske rabin gemun kowannensu, ya yayyage rigunarsu daidai ɗuwawu, sa’an nan ya sallame su.
Da tog Hanun Davids Folk og lod det halve af deres Skæg afrage og Halvdelen af deres Klæder skære af til Sædet, og derpå lod han dem gå.
5 Sa’ad da aka gaya wa Dawuda game da wannan, sai ya aiki manzanni su taryi waɗannan mutanen da aka ci mutuncinsu, gama an wulaƙanta su ƙwarai. Sai sarki ya ce musu, “Ku dakata a Yeriko har sai gemunku ya sāke girma, sa’an nan ku dawo.”
Da David fik Efterretning herom, sendte han dem et Bud i Møde, thi Mændene var blevet grovelig forhånet; og Kongen lod sige: "Bliv i Jeriko, til eders Skæg er vokset ud!"
6 Da Ammonawa suka gane cewa Dawuda ya ji fushi da su sosai saboda abin da suka yi, sai suka yi hayar sojojin ƙasar Arameyawa dubu ashirin daga Bet Rehob da Aram-Zoba, suka kuma yi hayar sarkin Ma’aka tare da mutum dubu ɗaya, suka kuma yi hayar maza dubu goma sha biyu daga Tob.
Men da Ammoniterne så, at de havde lagt sig for Had hos David, sendte de Bud og lejede Aramæerne fra Bef-Rehob og Zoba, 20000 Mand Fodfolk, Kongen af Ma'aka med 1000 Mand og Folkene fra Tob, 12000 Mand.
7 Da jin haka, Dawuda ya tura Yowab da dukan sojojin yaƙi.
Da David hørte det, sendte han Joab af Sted med hele Hæren og Kærnetropperne.
8 Ammonawa suka fita suka ja dāgār yaƙi a ƙofar shiga birninsu, yayinda Aram-Zoba, da na Rehob, da mutane Tob, da kuma na Ma’aka, suka ja tasu dāgār a karkara.
Ammoniterne rykkede så ud og stillede sig op til Kamp lige uden for Porten, medens Aramæerne fra Zoba og Rehob og Mændene fra Tob og Ma'aka stod for sig selv på åben Mark.
9 Yowab ya ga cewa an ja masa dāgār yaƙi gaba da baya; saboda haka sai ya zaɓi waɗansu shahararrun sojoji cikin Isra’ila, ya sa su gabza da Arameyawa.
Da Joa så, at Angreb truede ham både forfra og bagfra, gjorde han et Udvalg blandt alt Israels udsøgte Mandskab og tog Stilling over for Aramæerne,
10 Ya sa sauran mutanen a ƙarƙashin Abishai ɗan’uwansa, ya sa su gabza da Ammonawa.
medens han overlod Resten af Mandskabet til sin Broder Abisjaj, som tog Stilling over for Ammoniterne.
11 Yowab ya ce, “In Arameyawa suka fi ƙarfina, sai ku kawo mini gudummawa; amma in Ammonawa suka fi ƙarfinku, sai mu kawo muku gudummawa.
Og han sagde: "Hvis Aramæerne bliver mig for stærke, skal du ile mig til Hjælp; men bliver Ammoniterne dig for stærke, skal jeg komme og hjælpe dig.
12 Ku yi ƙarfin hali, mu kuma yi yaƙi da ƙarfin zuciya saboda mutanenmu da kuma birane Allahnmu. Ubangiji zai yi abin da yake da kyau a idanunsa.”
Tag Mod til dig og lad os tappert værge vort Folk og vor Guds Byer - så får HERREN gøre, hvad ham tykkes godt!"
13 Sa’an nan Yowab da rundunar da take tare da shi suka ci gaba don su gabza da Arameyawa, Arameyawa kuwa suka gudu a gabansa.
Derpå rykkede Joab frem med sine Folk til Kamp mod Aramæerne, og de flygtede for ham.
14 Da Ammonawa suka ga Arameyawa suna gudu, sai su ma suka ruga da gudu a gaban Abishai, suka shiga cikin birni. Sa’an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙin da ya yi da Ammonawa.
Og da Ammoniterne så, at Aramæerne tog Flugten, flygtede de for Abisjaj og trak sig ind i Byen. Derpå vendte Joab tilbage fra Kampen med Ammoniterne og kom til Jerusalem.
15 Bayan Arameyawa suka ga Isra’ila ta ci su da yaƙi, sai suka sāke tattara kansu.
Men da Aramæerne så, at de var slået af Israel, samlede de sig,
16 Hadadezer sarkin Zoba ya aika a kawo Arameyawan da suke ƙetaren Kogin Yuferites. Suka iso Helam a ƙarƙashin shugabancin Shobak, shugaban dukan sojojin Hadadezer.
og Hadad'ezer sendte Bud og lod Aramæerne hinsides Floden rykke ud, og de kom til Helam med Sjobak, Hadad'ezers Hærfører, i Spidsen.
17 Da aka gaya wa Dawuda wannan, sai ya tattara dukan Isra’ila, ya ƙetare Urdun, ya je Helam. Arameyawa suka ja dāgār yaƙinsu, suka kara da Dawuda.
Da David fik Efterretning herom, samlede han hele Israel, satte over Jordan og kom til Helam, hvor Aramæerne stillede sig op til Kamp mod David og angreb ham.
18 Amma Arameyawa suka gudu a gaban Isra’ila, Dawuda kuwa ya kashe mahayan keken yaƙinsu ɗari bakwai, da sojojin ƙasa dubu arba’in. Ya bugi Shobak, shugaban ƙungiyar sojansu ya kuwa mutu a can.
Men Aramæerne flygtede for Israel, og David nedhuggede 700 Stridsheste og 40000 Mand af Aram; også deres Hærfører Sjobak slog han ihjel der.
19 Sa’ad da dukan sarakuna waɗanda suke abokan tarayya na Hadadezer suka ga Isra’ila sun ci su da yaƙi, sai suka yi sulhu da Isra’ilawa, suka kuma zama bayinsu. Wannan ya sa Arameyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudummawa.
Da alle Hadad'ezers Lydkonger så, at de var slået af Israel, sluttede de Fred med Israel og underkastede sig. Og Aramæerne vovede ikke at hjælpe Ammoniterne mere.

< 2 Sama’ila 10 >