< 1 Sama’ila 24 >

1 Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
Pripetilo se je, ko se je Savel vrnil iz zasledovanja Filistejcev, da mu je bilo povedano, rekoč: »Glej, David je v divjini En Gedi.«
2 Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
Potem je Savel vzel tri tisoč izbranih mož iz vsega Izraela in odšel, da poišče Davida in njegove ljudi na skalah divjih koz.
3 Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
Ob poti je prišel k stajam za ovce, kjer je bila votlina in Savel je šel noter, da pokrije svoja stopala. David in njegovi možje pa so ostajali ob straneh votline.
4 Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
Davidovi možje so mu rekli: »Glej, dan, o katerem ti je rekel Gospod: ›Glej, tvojega sovražnika bom izročil v tvojo roko, da mu boš lahko storil, kakor se ti zdi dobro.‹« Potem je David vstal in na skrivnem odsekal krajec Savlovega svečanega oblačila.
5 Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
Pripetilo se je potem, da ga je Davidovo srce udarilo, ker je odsekal krajec Savlovega oblačila.
6 Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
Svojim možem je rekel: » Gospod ne daj, da bi storil tako stvar svojemu gospodarju, Gospodovemu maziljencu, da iztegnem svojo roko zoper njega, ker je maziljen od Gospoda.«
7 Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
Tako je David s temi besedami zadržal svoje služabnike in jim ni pustil, da vstanejo zoper Savla. Toda Savel je vstal iz votline in odšel na svojo pot.
8 Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
Potem je tudi David vstal in šel ven iz votline in zaklical za Savlom, rekoč: »Moj gospod kralj.« Ko je Savel pogledal za seboj, se je David sklonil s svojim obrazom k zemlji in se priklonil.
9 Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
David je rekel Savlu: »Zakaj poslušaš besede ljudi, govoreč: ›Glej, David išče tvoje zlo?‹
10 Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
Glej, ta dan so tvoje oči videle, kako te je Gospod v votlini izročil v mojo roko. Nekateri so mi zaukazali, naj te usmrtim, toda moje oko ti je prizaneslo. Rekel sem: ›Ne bom iztegnil svoje roke zoper svojega gospoda, kajti on je Gospodov maziljenec.‹
11 Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
Poleg tega, moj oče, glej, da, poglej krajec svojega svečanega oblačila v moji roki, kajti v tem, da sem odsekal krajec tvojega svečanega oblačila in te nisem usmrtil, vedi in vidi, da v moji roki ni niti zla niti prestopka in nisem grešil zoper tebe, vendar ti loviš mojo dušo, da jo vzameš.
12 Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
Gospod sodi med menoj in teboj in Gospod naj me maščuje nad teboj, toda moja roka ne bo nad teboj.
13 Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
Kakor pravi pregovor starcev: ›Zlobnost izvira od zlobnih, ‹ toda moja roka ne bo nad teboj.
14 “Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
Za kom je Izraelov kralj prišel ven? Za kom tečeš? Za mrtvim psom, za bolho.
15 Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
Gospod naj bo torej sodnik in sodi med menoj in teboj in gleda in zagovarja mojo pravdo in me osvobodi iz tvoje roke.«
16 Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
Pripetilo se je, ko je David Savlu prenehal govoriti te besede, da je Savel rekel: » Ali je to tvoj glas, moj sin David?« Savel je povzdignil svoj glas in zajokal.
17 Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
Davidu je rekel: »Pravičnejši si kakor jaz, kajti nagradil si mi dobro, medtem ko sem ti jaz nagradil zlo.
18 Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
Danes si pokazal, kako dobro si ravnal z menoj, ker ko me je Gospod izročil v tvojo roko, me nisi ubil.
19 In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
Kajti če človek najde svojega sovražnika ali ga bo pustil sproščeno oditi? Zato [naj] te Gospod dobro nagradi za to, kar si mi ta dan storil.
20 Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
Sedaj glej, dobro vem, da boš zagotovo postal kralj in da bo Izraelovo kraljestvo utrjeno v tvoji roki.
21 Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
Prisezi mi torej sedaj pri Gospodu, da ne boš iztrebil mojega semena za menoj in da ne boš uničil mojega imena iz hiše mojega očeta.«
22 Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.
David je prisegel Savlu. Savel je odšel domov, toda David in njegovi možje so se povzpeli na utrjen kraj.

< 1 Sama’ila 24 >