< 1 Sama’ila 17 >

1 To, fa, Filistiyawa suka tattara mayaƙansu suka haɗu a Soko cikin Yahuda domin yaƙi. Suka yi sansani a Efes-Dammim, tsakanin Soko da Azeka.
AmaFilisti asebuthela amabutho awo impi; abuthana eSoko engeyakoJuda, amisa inkamba phakathi kweSoko leAzeka, eEfesi-Damimi.
2 Shawulu da Isra’ilawa suka taru suka yi sansani a Kwarin Ela suka ja dāgā don su yi yaƙi da Filistiyawa.
USawuli lamadoda akoIsrayeli babuthana, bamisa inkamba esigodini seEla, bahlela impi ukumelana lamaFilisti.
3 Filistiyawa suka zauna a tudu guda, Isra’ilawa kuma suka zauna a ɗaya tudun. Kwari yana a tsakaninsu.
AmaFilisti asesima entabeni ngapha, loIsrayeli wema entabeni ngale, lesigodi sasiphakathi kwabo.
4 Wani jarumin da ake kira Goliyat wanda ya fito daga Gat, ya fita daga sansanin Filistiyawa. Tsawonsa ya fi ƙafa tara.
Kwasekuphuma enkambeni yamaFilisti iqhawe; ibizo lalo lalinguGoliyathi weGathi; ubude balo babuyizingalo eziyisithupha lokwelulwa kweminwe.
5 Ya sa hular kwanon da aka yi da tagulla, da rigar ƙarfe mai sulke, nauyin rigar ya kai shekel dubu biyar.
Kwakulekhowa lethusi ekhanda lalo; laligqoke ibhatshi lensimbi elilamaxolo; njalo isisindo sebhatshi lensimbi sasingamashekeli ethusi ayizinkulungwane ezinhlanu.
6 A ƙafafunsa kuwa ya sa ƙarafar tagulla, rataye a bayansa kuma māshi ne na tagulla.
Njalo kwakulemigwamazi yethusi emibaleni yalo, lomkhonto wethusi phakathi laphakathi kwamahlombe alo.
7 Ƙotar kibiyarsa kuwa kamar sandar saƙar igiya take, ƙarfen kibiyar kuma nauyinsa ya kai shekel ɗari shida. Mai riƙe masa garkuwa yana tafe a gabansa.
Loluthi lomkhonto walo lwalunjengogodo lomaluki, lengqamu yomkhonto walo yayingamashekeli ensimbi angamakhulu ayisithupha; lophatha isihlangu esikhulu wayehamba phambi kwalo.
8 Goliyat ya tsaya ya tā da murya wa hafsoshin Isra’ila ya ce, “Me ya sa kuka fito kuna layi don yaƙi? Ni ba Bafilistin ba ne? Ku kuma ba bayin Shawulu ba ne? Ku zaɓi waninku yă zo nan.
Lema, lamemeza emaviyweni akoIsrayeli lathi kuwo: Liphumelani ukuzahlela impi? Kangisuye umFilisti yini, lani izinceku zikaSawuli? Zikhetheleni umuntu ehlele kimi.
9 In zai iya yin faɗa har yă kashe ni, to, za mu zama bayinku. Amma in na fi ƙarfinsa na kashe shi, to, sai ku zama bayinmu, ku kuma yi mana bauta.”
Uba elakho ukulwa lami angibulale, sizakuba yizigqili zenu; kodwa uba mina ngimehlula ngimbulale, lizakuba yizigqili zethu, lisisebenzele.
10 Sai Bafilistin ya ce, “A wannan rana, na kalubalanci sojojin Isra’ila, ku ba ni mutum ɗaya mu yi faɗa.”
UmFilisti wasesithi: Mina ngiyaweyisa amaviyo akoIsrayeli lamuhla; nginikani indoda ukuze silwisane.
11 Da jin maganganun Bafilistin, sai Shawulu da dukan Isra’ila suka damu suka kuma ji tsoro.
Lapho uSawuli loIsrayeli wonke besizwa lamazwi omFilisti, batshaywa luvalo, besaba kakhulu.
12 To, Dawuda dai ɗan wani mutumin Efratawa ne mai suna Yesse, shi mutumin Betlehem ne a cikin Yahudiya. Yesse yana da yara maza takwas, a zamanin Shawulu kuwa, Yesse ya riga ya tsufa.
UDavida wayeyindodana yalowomEfrathi weBhethelehema-Juda, obizo lakhe lalinguJese; wayelamadodana ayisificaminwembili. Njalo lowomuntu wahamba njengomuntu omdala phakathi kwamadoda ensukwini zikaSawuli.
13 Manyan’ya’yansa maza uku, sun bi Shawulu wajen yaƙi. Ɗansa na fari shi ne Eliyab, na biyu shi ne Abinadab, na uku kuwa shi ne Shamma.
Asehamba amadodana amathathu kaJese amadala, amlandela uSawuli empini. Lamabizo amadodana akhe amathathu ayeyile empini ayenguEliyabi izibulo, lowesibili wakhe uAbinadaba, lowesithathu uShama.
14 Dawuda shi ne ɗan autansu. Manyan’yan mazan nan uku suka bi Shawulu.
Njalo uDavida nguye owayelicinathunjana; lamathathu amadala alandela uSawuli.
15 Amma Dawuda yakan tafi sansanin Shawulu lokaci-lokaci yă kuma koma Betlehem don yă yi kiwon tumakin mahaifinsa.
Kodwa uDavida wahamba wabuyela esuka kuSawuli ukuyakwelusa izimvu zikayise eBhethelehema.
16 Kwana arba’in cif, Bafilistin nan ya yi ta fitowa kowane safe da kuma kowace yamma.
UmFilisti wayesondela-ke ekuseni kakhulu lantambama ezimisa okwensuku ezingamatshumi amane.
17 Yesse ya ce wa ɗansa Dawuda, “Ka ɗauki wannan gasasshen hatsi da waɗannan curin burodi goma, ka kai wa’yan’uwanka a sansani da sauri.
UJese wasesithi kuDavida indodana yakhe: Ake uthathele abafowenu i-efa lamabele akhanzingiweyo, lalezizinkwa ezilitshumi, ugijimele enkambeni kubafowenu.
18 Ka haɗa da waɗannan cuku guda goma, ka kai wa komandan rundunarsu. Ka ga lafiyar’yan’uwanka, ka kawo mini labari daga wurinsu.
Laleziziqa zetshizi ezilitshumi uziphathele induna yenkulungwane; ubone impilakahle yabafowenu, uthathe isibambiso kibo.
19 Suna tare da Shawulu da kuma dukan mutanen Isra’ila a Kwarin Ela, suna can suna yaƙi da Filistiyawa.”
Njalo uSawuli, labo, lawo wonke amadoda akoIsrayeli babesesigodini seEla besilwa lamaFilisti.
20 Kashegari da sassafe, Dawuda ya tashi ya bar tumakinsa wa wani yă lura da su, sai ya ɗauki kayansa, ya kama hanya kamar yadda Yesse ya umarce shi. Ya isa sansanin daidai sa’ad da rundunar tana fitowa zuwa bakin dāgā, suna kirarin yaƙi.
UDavida wasevuka ekuseni kakhulu, watshiya izimvu kumlindi, wakuthatha wahamba njengokulaywa kwakhe nguJese. Wafika enqabeni yezinqola lapho ibutho liphuma ngamaviyo, bememezela impi.
21 Isra’ila da Filistiyawa suka ja dāgā suna fuskantar junansu.
Njalo uIsrayeli lamaFilisti bahlela iviyo laqondana leviyo.
22 Dawuda ya bar kayansa a wajen wani mai lura da kaya, sai ya ruga zuwa bakin dāgā yă gai da’yan’uwansa.
UDavida wasetshiya impahla ezisuka kuye ngaphansi kwesandla somlindi wempahla, wagijimela eviyweni wafika wabuza abafowabo impilakahle.
23 Da yana magana da su sai Goliyat, jarumin nan Bafilistin daga Gat ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya tā da murya kamar yadda ya saba. Dawuda kuwa ya ji shi.
Esakhuluma labo, khangela, iqhawe lenyuka, ibizo lalo lalinguGoliyathi, umFilisti weGathi, laphuma emaviyweni amaFilisti, lakhuluma njengokwalawomazwi; loDavida wawezwa.
24 Da Isra’ilawa suka ga mutumin, sai dukansu suka gudu saboda tsananin tsoro.
Njalo wonke amadoda akoIsrayeli athi embona lowomuntu ambalekela, esaba kakhulu.
25 Isra’ilawa suka yi ta cewa, “Kun ga yadda wannan mutum yana ta fitowa? Yana fitowa ne don yă kalubalanci Isra’ila. Sarki zai sāka wa mutumin da ya kashe wannan da dukiya mai yawa. Zai kuma ba shi’yarsa yă aura, yă cire suna mahaifinsa daga biyan kuɗin haraji cikin Isra’ila.”
Amadoda akoIsrayeli athi-ke: Limbonile lowana umuntu owenyukileyo yini? Ngoba wenyukele ukweyisa uIsrayeli. Kuzakuthi-ke indoda ezambulala, inkosi izayinothisa ngenotho enkulu, iyinike lendodakazi yayo, lendlu kayise izayenza ikhululeke koIsrayeli.
26 Dawuda ya tambayi mutanen da suke tsaye kusa da shi ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilistin nan, ya kuma cire wannan kunya daga Isra’ila? Wane ne wannan bafilistin marar kaciya da yake kalubalantar rundunar yaƙi na Allah mai rai?”
UDavida wasekhuluma emadodeni ayemi laye esithi: Kuzakwenziwani endodeni ebulala lumFilisti, isuse ihlazo koIsrayeli? Ngoba ungubani lumFilisti ongasokanga ukuthi aweyise amaviyo kaNkulunkulu ophilayo?
27 Sai suka sāke gaya masa abin da suka faɗa cewa, “Ga abin da zai faru da wanda ya kashe shi.”
Abantu basebemphendula njengalelolizwi besithi: Kuzakwenziwa njalo endodeni embulalayo.
28 Da wansa Eliyab, ya ji yana magana da mutanen, sai ransa ya ɓace ƙwarai saboda fushi, sai ya ce wa Dawuda, “Me ka zo yi a nan? Wa kuma ka bar wa’yan tumakin a jeji? Na san ka da taurinkai, da kuma mugun hali. Ka zo nan ne don ka yi kallon yaƙi kawai.”
UEliyabi umnewabo omdala wezwa-ke lapho ekhuluma lamadoda; lentukuthelo kaEliyabi yavuthela uDavida, wathi: Wehleleleni lapha? Izimvu leziyana ezinlutshwana uzitshiye lobani egangeni? Mina ngiyakwazi ukuziqhenya kwakho lobubi benhliziyo yakho; ngoba wehlele ukubona impi.
29 Dawuda ya ce, “To, yanzu me na yi? Ba zan ma yi magana ba?”
Kodwa uDavida wathi: Sengenzeni? Bekungasilizwi nje yini?
30 Sai ya juya wajen wani kuma ya sāke kawo zancen, mutanen kuwa suka amsa masa kamar dā.
Wasemfulathela, waya komunye, wakhuluma laye njengokwalelolizwi; abantu basebebuyisela impendulo kuye njengelizwi lakuqala.
31 Aka ji abin da Dawuda ya ce, aka kuwa gaya wa Shawulu, Shawulu kuma ya aika a kawo shi.
Lapho sebewezwile amazwi uDavida awakhulumayo, bawakhuluma phambi kukaSawuli; wasememukela.
32 Da Shawulu ya tambayi Dawuda, sai Dawuda ya ce masa, “Kada kowa yă damu saboda wannan Bafilistin. Bawanka zai je yă yi faɗa da shi.”
UDavida wasesithi kuSawuli: Kakungehluleki inhliziyo yomuntu ngenxa yakhe; inceku yakho izahamba iyekulwa lalowomFilisti.
33 Shawulu ya ce, “Ba za ka iya yin faɗa da wannan Bafilistin ba, ya daɗe yana yaƙi, ya yi yaƙi tun yana saurayi. Ga shi kuwa kai ɗan yaro ne kawai.”
Kodwa uSawuli wathi kuDavida: Ungeke waya kulumFilisti ukulwa laye; ngoba wena ungumfana, yena-ke uyindoda yempi kusukela ebutsheni bakhe.
34 Amma Dawuda ya ce wa Shawulu, “Bawanka yana kiwon tumakin mahaifinsa. Sa’ad da zaki ko beyar ta zo ta kama tunkiya, ta tafi da ita.
Kodwa uDavida wathi kuSawuli: Inceku yakho yayiselusa izimvu zikayise; lapho kwafika isilwane lebhere, kwathatha imvu emhlanjini,
35 Nakan bi ta a baya in buga ta in kuma ƙwato tunkiyar daga bakinta. In kuma ta taso mini, nakan cafke ta a gashinta in buga ta in kashe.
ngaphuma ngakulandela, ngakutshaya, ngayikhulula emlonyeni wakho; lapho kungivukela, ngakubamba ngendevu, ngakutshaya, ngakubulala.
36 Bawanka ya kashe zaki da beyar, wannan Bafilistin marar kaciya zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, domin ya rena rundunar Allah mai rai.
Inceku yakho yabulala kokubili isilwane lebhere; lalo umFilisti ongasokanga uzakuba njengokunye kwakho, lokhu eyise amaviyo kaNkulunkulu ophilayo.
37 Ubangiji wanda ya cece ni daga kumbar zaki da kuma kumbar beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafilistin.” Shawulu ya ce wa Dawuda, “Je ka, Ubangiji yă kasance tare da kai.”
UDavida wathi futhi: INkosi eyangophula kuzipho lwesilwane lakuzipho lwebhere, yona izangophula esandleni salo umFilisti. USawuli wasesithi kuDavida: Hamba, leNkosi kayibe lawe.
38 Sai Shawulu ya kawo kayan yaƙinsa ya sa wa Dawuda. Ya sa masa hular kwanon da aka yi da tagulla a kansa, ya kuma sa masa rigar ƙarfensa.
USawuli wasegqokisa uDavida izigqoko zakhe, wafaka ikhowa lethusi ekhanda lakhe, wamgqokisa ibhatshi lensimbi.
39 Dawuda ya ɗaura māshin Shawulu a sulken, ya yi ƙoƙari yă zaga, sai ya ji ba zai iya ba saboda bai saba ba. Ya cewa Shawulu, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, domin ban saba ba.” Don haka ya tuɓe su.
UDavida wasebhinca inkemba yakhe phezu kwezigqoko zakhe, walinga ukuhamba, ngoba wayengakuzamanga. UDavida wasesithi kuSawuli: Kangilakho ukuhamba ngilalezizinto ngoba kangizizamanga. UDavida wasezikhumula kuye.
40 Sai ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya sa su a’yar jakarsa ta makiyaya; ya kuma ɗauki majajjawarsa, ya tafi, yă fuskanci Bafilistin.
Wasethatha umqwayi wakhe esandleni sakhe, wazikhethela amatshe amahlanu abutshelezi esifuleni, wawafaka esikhwameni sikamelusi ayelaso, ngitsho emxhakeni, lesavutha sakhe sasisesandleni sakhe, wasesondela kumFilisti.
41 Ana ciki haka, sai Bafilistin nan shi ma ya fita yana gusowa zuwa wurin Dawuda. Mai riƙe masa garkuwar yaƙi kuwa yana tafe a gabansa.
UmFilisti wasehamba waya wasondela kuDavida; lomuntu ophethe isihlangu esikhulu wayephambi kwakhe.
42 Bafilistin ya dubi Dawuda daga sama har ƙasa, ya gan dai ɗan yaro ne kawai, kyakkyawa kuma mai ƙoshin lafiya, sai ya rena shi.
Kwathi umFilisti ekhangela ebona uDavida, wameyisa; ngoba wayengumfana njalo ebomvana elobuso obubukekayo.
43 Ya ce masa, “Kana tsammani ni kare ne da za ka zo mini da sanda?” Sai ya la’anci Dawuda da sunayen allolin Filistiyawa.
UmFilisti wasesithi kuDavida: Ngiyinja yini ukuthi wena uze kimi ulezinduku? UmFilisti wasemqalekisa uDavida ngabonkulunkulu bakhe.
44 Ya ce, “Zo nan, ni kuwa zan ba da naman jikinka ga tsuntsayen sama da namun jeji su ci.”
UmFilisti wasesithi kuDavida: Woza kimi, ngizanika inyoni zamazulu lenyamazana zeganga inyama yakho.
45 Dawuda ya ce wa Bafilistin, “Kana zuwa ka yaƙe ni da māshi da takobi da kere, amma ni ina zuwa in yaƙe ka a cikin sunan Ubangiji Maɗaukaki, Allah na rundunar Isra’ila, wanda ka rena.
UDavida wasesithi kumFilisti: Wena uza kimi ulenkemba, lomkhonto, lomdikadika; kodwa mina ngiza kuwe ngebizo leNkosi yamabandla, uNkulunkulu wamaviyo akoIsrayeli omeyisileyo.
46 Yau nan, Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan kuwa kashe ka, in datse kanka. Yau, zan ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namun jeji, da haka duniya za tă sani lalle akwai Allah a cikin Isra’ila.
Lamuhla iNkosi izakuvalela esandleni sami, ngizakutshaya, ngisuse ikhanda lakho kuwe; nginike lamuhla inyoni zamazulu lenyamazana zomhlaba izidumbu zebutho lamaFilisti, ukuze umhlaba wonke wazi ukuthi kukhona uNkulunkulu koIsrayeli.
47 Duk waɗanda suka taru a nan za su san cewa ba da māshi ko takobi ne Ubangiji yake ceto ba, gama yaƙin nan na Ubangiji ne, shi kuwa zai bashe ku duka a hannuwanmu.”
Lalelibandla lonke lizakwazi ukuthi iNkosi kayisindisi ngenkemba langomkhonto; ngoba impi ngeyeNkosi, njalo izalinikela esandleni sethu.
48 Yayinda Bafilistin yana matsowa kusa domin yă fāɗa wa Dawuda, sai Dawuda ya ruga a guje zuwa bakin dāgā don yă same shi.
Kwasekusithi lapho umFilisti esukuma ehamba esondela ukuhlangabeza uDavida, uDavida wasephangisa wagijimela ngaseviyweni ukuhlangana lomFilisti.
49 Ya sa hannu a jakarsa ya ɗauki dutse, ya sa cikin majajjawa ya wurga, dutsen kuwa ya bugi Bafilistin a goshi, dutsen ya shiga cikin goshinsa, sai Bafilistin ya fāɗi rubda ciki.
UDavida wasefaka isandla sakhe esikhwameni, wakhupha khona ilitshe, walijikijela, wamtshaya umFilisti ebunzini lakhe ilitshe laze latshona ebunzini lakhe, wawela emhlabathini ngobuso bakhe.
50 Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara a kan Bafilistin. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba.
Ngalokho uDavida wamehlula umFilisti ngesavutha langelitshe, wamtshaya umFilisti, wambulala; kodwa kwakungelankemba esandleni sikaDavida.
51 Dawuda ya ruga ya tsaya a bisan Bafilistin, ya zare takobin Bafilistin daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka juya suka gudu.
Ngakho uDavida wagijima wema phezu komFilisti, wathatha inkemba yakhe, wayihwatsha esikhwameni sayo, wambulala, waquma ikhanda lakhe ngayo. Lapho amaFilisti ebona ukuthi iqhawe lawo selifile, abaleka.
52 Mutanen Isra’ila da na Yahuda suka rugo gaba da babbar murya, suka fafari Filistiyawa har zuwa mashigin Gat da kuma ƙofofin Ekron. Gawawwakin Filistiyawa suka bazu a hanyar Sha’arayim zuwa Gat da kuma Ekron.
Lamadoda akoIsrayeli lawakoJuda asukuma amemeza, axotshana lamaFilisti uze uyefika esigodini lemasangweni eEkhironi. Labalimeleyo bamaFilisti bawela endleleni yeShaharayimi kuze kube seGathi njalo kuze kube seEkhironi.
53 Da Isra’ilawa suka komo daga bin Filistiyawa sai suka washe sansanin Filistiyawa.
Abantwana bakoIsrayeli basebephenduka ekuxotshaneni ngamandla lamaFilisti, baphanga inkamba zawo.
54 Dawuda ya ɗauki kan Bafilistin zuwa Urushalima. Sai Dawuda ya ajiye kayan yaƙin Bafilistin a tentinsa.
UDavida wasethatha ikhanda lomFilisti, waliletha eJerusalema; kodwa wabeka izikhali zakhe ethenteni lakhe.
55 Yayinda Shawulu yake kallon Dawuda sa’ad da za shi yă yaƙi Bafilistin, sai ya tambayi Abner, komandan rundunarsa ya ce, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya ce ran sarki yă daɗe, “Ban sani ba.”
Lapho uSawuli ebona uDavida ephuma ukuyahlangabeza umFilisti, wathi kuAbhineri induna yebutho: Uyindodana kabani lumfana Abhineri? UAbhineri wasesithi: Kuphila komphefumulo wakho, nkosi, kangazi.
56 Sarki ya ce, “Ka tambaya mini ko yaron wane ne wannan saurayi.”
Inkosi yasisithi: Buza wena ukuthi liyindodana kabani lelijaha.
57 Dawuda yana dawowa daga karkashe Filistiyawa ke nan, sai Abner ya kai shi gaban Shawulu, riƙe da kan Bafilistin.
Lapho uDavida esephendukile ekubulaleni umFilisti, uAbhineri wamthatha, wamusa phambi kukaSawuli elekhanda lomFilisti esandleni sakhe.
58 Sai Shawulu ya ce, “Kai ɗan wane ne, saurayi?” Dawuda ya ce, “Ni ɗan bawanka Yesse ne, na Betlehem.”
USawuli wasesithi kuye: Uyindodana kabani, jaha? UDavida wasesithi: Ngiyindodana yenceku yakho uJese umBhethelehema.

< 1 Sama’ila 17 >