< 1 Sarakuna 14 >

1 A lokacin Abiya, ɗan Yerobowam ya kamu da ciwo,
At that time Abijah son of Jeroboam became very sick.
2 sai Yerobowam ya ce wa matarsa, “Ki tafi, ki ɓad da kama, don kada a gane ke a matsayin matar Yerobowam. Ki je Shilo. Annabi Ahiya yana a can, wannan wanda ya ce mini zan zama sarki a bisa wannan mutane.
Jeroboam said to his wife, “Please arise and disguise yourself, so you will not be recognized as my wife, and go to Shiloh, because Ahijah the prophet is there; he is the one who spoke about me, saying that I would become king over these people.
3 Ki ɗauki dunƙulen burodi goma tare da ke, da waina, da tulun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.”
Take with you ten loaves, some cakes, and a jar of honey, and go to Ahijah. He will tell you what will happen to the child.”
4 Saboda haka matar Yerobowam ta yi abin da ya faɗa, ta kuma tafi gidan Ahiya a Shilo. Yanzu dai Ahiya ba ya gani; idanunsa sun tafi saboda tsufa.
Jeroboam's wife did so; she left and went to Shiloh and came to the house of Ahijah. Now Ahijah could not see; he lost his sight because of old age.
5 Amma Ubangiji ya ce wa Ahiya, “Matar Yerobowam tana zuwa tă tambaye ka game da ɗanta, gama yana ciwo, za ka kuwa ba ta amsa kaza da kaza. Sa’ad da ta iso za tă yi kamar wata ce dabam.”
Yahweh said to Ahijah, “Look, the wife of Jeroboam is coming to seek advice from you regarding her son, for he is sick. Say such and such to her, because when she comes, she will act as if she were some other woman.”
6 Saboda haka sa’ad da Ahiya ya ji motsin sawunta a ƙofa, sai ya ce, “Ki shigo, matar Yerobowam. Me ya sa kike yi kamar wata ce dabam? An aiko ni wurinki da labari marar daɗi.
When Ahijah heard the sound of her feet as she came in at the door, he said, “Come in, wife of Jeroboam. Why do you pretend to be someone you are not? I have been sent to you with bad news.
7 Je ki faɗa wa Yerobowam cewa ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Na tā da kai daga cikin mutane, na mai da kai shugaba a bisa mutanena Isra’ila.
Go, tell Jeroboam that Yahweh, the God of Israel, says, 'I raised you from among the people to make you the leader over my people Israel.
8 Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba da shi gare ka, amma ba ka zama kamar bawana Dawuda wanda ya kiyaye umarnaina ya kuma bi ni da dukan zuciyarsa, yana yin abin da yake daidai kaɗai a idanuna ba.
I tore the kingdom away from the family of David and gave it to you, yet you have not been like my servant David, who kept my commandments and followed me with all his heart, to do only what was right in my eyes.
9 Ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka rayu kafin kai. Ka yi wa kanka waɗansu alloli, gumakan da aka yi da ƙarfe; ka tsokane ni na yi fushi, ka kuma juye mini baya.
Instead, you have done evil, more than all who were before you. You have made other gods, and you have cast metal images to provoke me to anger, and have thrust me behind your back.
10 “‘Saboda wannan, zan kawo masifa a gidan Yerobowam. Zan yanke kowane ɗa na ƙarshe a Isra’ila, bawa ko’yantacce. Zan ƙone gidan Yerobowam kamar yadda mutum yakan ƙone juji, sai duk ya ƙone ƙurmus.
Therefore, look, I will bring disaster on your family; I will cut off from you every male child in Israel, whether slave or free, and will completely remove your family, like someone who burns up dung until it is gone.
11 Karnuka za su ci waɗanda suka mutu na Yerobowam a cikin birni, kuma tsuntsayen sararin sama za su cinye waɗanda suka mutu a jeji. Ni Ubangiji na faɗa!’
Anyone who belongs to your family who dies in the city will be eaten by dogs, and anyone who dies in the field will be eaten by the birds of the heavens, for I, Yahweh, have said it.'
12 “Ke kuma, ki koma gida. Sa’ad da kika taka ƙafa a birninki, yaron zai mutu.
So arise, wife of Jeroboam, and go back to your home; when your feet enter the city, the child Abijah will die.
13 Dukan Isra’ila kuwa za su yi makoki dominsa. Shi ne kaɗai na Yerobowam wanda za a binne, domin shi ne kaɗai a gidan Yerobowam wanda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya sami wani ɗan abu mai kyau a kansa.
All Israel will mourn for him and bury him. He is the only one from Jeroboam's family who will go into a grave, because only in him, out of Jeroboam's house, was anything good found in the sight of Yahweh, the God of Israel.
14 “Ubangiji zai tā da wani sarki wa kansa a bisa Isra’ila wanda zai hallaka iyalin Yerobowam. Ko yanzu ma, wannan zai fara faruwa.
Also, Yahweh will raise up a king of Israel who will cut off the family of Jeroboam on that day. Today is that day, right now.
15 Ubangiji kuma zai bugi Isra’ila, har tă zama kamar kyauro mai girgiza a bakin rafi. Zai tumɓuke Isra’ila daga wannan ƙasa mai kyau da ya ba wa kakanninsu, yă watsar da su gaba da Kogin Yuferites domin sun tsokane Ubangiji har ya yi fushi, ta wurin yin ginshiƙan Ashera.
For Yahweh will attack Israel as a reed is shaken in the water, and he will root up Israel out of this good land that he gave to their ancestors. He will scatter them beyond the Euphrates River, because they have made their Asherah poles and provoked Yahweh to anger.
16 Zai kuma ba da Isra’ila saboda zunuban da Yerobowam ya yi, da ya kuma sa Isra’ila suka yi.”
He will give Israel up because of the sins of Jeroboam, the sins that he has committed, and through which he has led Israel to sin.”
17 Sai matar Yerobowam ta tashi ta tafi, ta kuwa tafi Tirza. Nan da nan da ta taka madogarar ƙofar gidan, sai yaron ya mutu.
So Jeroboam's wife arose and left, and came to Tirzah. As she came to the threshold of her house, the child died.
18 Suka binne shi, dukan Isra’ila kuwa suka yi makoki dominsa, yadda Ubangiji ya faɗa ta wurin bawansa annabi Ahiya.
All Israel buried him and mourned for him, just as it was told to them by the word of Yahweh which he had spoken by his servant Ahijah the prophet.
19 Sauran ayyukan sarautar Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, ba a rubuce suke a littafin tarihi na sarakunan Isra’ila ba?
As for the other matters concerning Jeroboam, how he waged war and how he reigned, see, they are written in the book of the events of the kings of Israel.
20 Ya yi mulki shekaru ashirin da biyu, sai ya huta tare da kakanninsa. Sai Nadab ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Jeroboam reigned twenty-two years and then slept with his ancestors, and Nadab his son became king in his place.
21 Rehobowam ɗan Solomon ya zama sarki a Yahuda. Yana da shekara arba’in da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki shekaru goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra’ila don yă sa Sunansa. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita mutuniyar Ammon ce.
Now Rehoboam son of Solomon was reigning in Judah. Rehoboam was forty-one years old when he became king, and he reigned seventeen years in Jerusalem, the city that Yahweh had chosen out of all the tribes of Israel in which to put his name. His mother's name was Naamah the Ammonite woman.
22 Yahuda ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Ta wurin zunuban da suka yi, sun tā da fushin kishinsa fiye da yadda kakanninsu suka yi.
Judah did what was evil in the sight of Yahweh; they provoked him to jealousy with the sins that they committed, more than everything that their fathers had done.
23 Sun kuma kafa wa kansu masujadai da suke kan tuddai, da a kan keɓaɓɓun duwatsu, suka kuma gina ginshiƙan Ashera a kowane tudu, da kuma a ƙarƙashin kowane duhuwar itace.
For they also built for themselves high places, stone pillars, and Asherah poles on every high hill and under every green tree.
24 Har ma akwai maza karuwai na masujada. Mutane suka sa kansu ga yin kowane abin ƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora kafin Isra’ilawa.
There were also cultic prostitutes in the land. They did the same despicable practices as the nations that Yahweh had driven out before the people of Israel.
25 A shekara ta biyar ta Sarki Rehobowam, Shishak sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi.
It happened in the fifth year of King Rehoboam that Shishak king of Egypt came up against Jerusalem.
26 Ya kwashe dukiyar haikalin Ubangiji da kuma dukiyar fadan sarki. Ya ɗauki kome, har da dukan garkuwoyi na zinariya da Solomon ya yi.
He took away the treasures in the house of Yahweh, and the treasures in the king's house. He took everything away; he also took all the shields of gold that Solomon had made.
27 Saboda haka sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla ya mayar da su. Ya kuma naɗa waɗannan shugabannin matsara ya sa su aiki a ƙofar zuwa fadan sarki.
King Rehoboam made shields of bronze in their place and entrusted them into the hands of the commanders of the guard, who guarded the doors to the king's house.
28 Duk sa’ad da sarki ya tafi wurin haikalin Ubangiji, matsara sukan riƙe garkuwoyinsu, daga baya kuma sai su mai da su ɗakin tsaro.
It happened that whenever the king entered the house of Yahweh, the guards would carry them; then they would bring them back into the guardhouse.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Rehobowam kuwa, da kuma dukan abin da ya yi, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
As for the other matters concerning Rehoboam, and all that he did, are they not written in the book of the events of the kings of Judah?
30 Aka ci gaba da yaƙe-yaƙe tsakanin Rehobowam da Yerobowam.
There was constant warfare between Rehoboam and Jeroboam.
31 Sai Rehobowam ya huta da kakanninsa, aka kuma binne shi tare da su a Birnin Dawuda. Sunan mahaifiyarsa Na’ama, ita kuwa mutuniyar Ammon ce. Sai Abiyam ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
So Rehoboam slept with his ancestors and was buried with them in the city of David. His mother's name was Naamah the Ammonite woman. Abijah his son became king in his place.

< 1 Sarakuna 14 >