< 1 Sarakuna 13 >

1 Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
And, behold, there came a man of God out of Judah by the word of the LORD unto Beth-el; and Jeroboam was standing by the altar to offer.
2 Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
And he cried against the altar by the word of the LORD, and said: 'O altar, altar, thus saith the LORD: Behold, a son shall be born unto the house of David, Josiah by name; and upon thee shall he sacrifice the priests of the high places that offer upon thee, and men's bones shall they burn upon thee.'
3 A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
And he gave a sign the same day saying: 'This is the sign which the LORD hath spoken: Behold, the altar shall be rent, and the ashes that are upon it shall be poured out.'
4 Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
And it came to pass, when the king heard the saying of the man of God, which he cried against the altar in Beth-el, that Jeroboam put forth his hand from the altar, saying: 'Lay hold on him.' And his hand, which he put forth against him, dried up, so that he could not draw it back to him.
5 Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
The altar also was rent, and the ashes poured out from the altar, according to the sign which the man of God had given by the word of the LORD.
6 Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
And the king answered and said unto the man of God: 'Entreat now the favour of the LORD thy God, and pray for me, that my hand may be restored me.' And the man of God entreated the LORD, and the king's hand was restored him, and became as it was before.
7 Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
And the king said unto the man of God: 'Come home with me, and refresh thyself, and I will give thee a reward.'
8 Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
And the man of God said unto the king: 'If thou wilt give me half thy house, I will not go in with thee, neither will I eat bread nor drink water in this place.
9 Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
For it so was charged me by the word of the LORD, saying: Thou shalt eat no bread, nor drink water, neither return by the way that thou camest.'
10 Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
So he went another way, and returned not by the way that he came to Beth-el.
11 To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
Now there dwelt an old prophet in Beth-el; and one of his sons came and told him all the works that the man of God had done that day in Beth-el, and the words which he had spoken unto the king, and they told them unto their father.
12 Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
And their father said unto them: 'What way went he?' For his sons had seen what way the man of God went, that came from Judah.
13 Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
And he said unto his sons: 'Saddle me the ass.' So they saddled him the ass; and he rode thereon.
14 Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
And he went after the man of God, and found him sitting under a terebinth; and he said unto him: 'Art thou the man of God that camest from Judah?' And he said: 'I am.'
15 Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
Then he said unto him: 'Come home with me, and eat bread.'
16 Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
And he said: 'I may not return with thee, nor go in with thee; neither will I eat bread nor drink water with thee in this place.
17 An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
For it was said to me by the word of the LORD: Thou shalt eat no bread nor drink water there, nor turn back to go by the way that thou camest.'
18 Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
And he said unto him: 'I also am a prophet as thou art; and an angel spoke unto me by the word of the LORD, saying: Bring him back with thee into thy house, that he may eat bread and drink water.' — He lied unto him. —
19 Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
So he went back with him, and did eat bread in his house, and drank water.
20 Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
And it came to pass, as they sat at the table, that the word of the LORD came unto the prophet that brought him back.
21 Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
And he cried unto the man of God that came from Judah, saying: 'Thus saith the LORD: Forasmuch as thou hast rebelled against the word of the LORD, and hast not kept the commandment which the LORD thy God commanded thee,
22 Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
but camest back, and hast eaten bread and drunk water in the place of which He said to thee: Eat no bread, and drink no water; thy carcass shall not come unto the sepulchre of thy fathers.'
23 Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
And it came to pass, after he had eaten bread, and after he had drunk, that he saddled for him the ass, namely, for the prophet whom he had brought back.
24 Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
And when he was gone, a lion met him by the way, and slew him; and his carcass was cast in the way, and the ass stood by it; the lion also stood by the carcass.
25 Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
And, behold, men passed by, and saw the carcass cast in the way, and the lion standing by the carcass; and they came and told it in the city where the old prophet dwelt.
26 Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
And when the prophet that brought him back from the way heard thereof, he said: 'It is the man of God, who rebelled against the word of the LORD; therefore the LORD hath delivered him unto the lion, which hath torn him, and slain him, according to the word of the LORD, which He spoke unto him.'
27 Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
And he spoke to his sons, saying: 'Saddle me the ass.' And they saddled it.
28 Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
And he went and found his carcass cast in the way, and the ass and the lion standing by the carcass; the lion had not eaten the carcass, nor torn the ass.
29 Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
And the prophet took up the carcass of the man of God, and laid it upon the ass, and brought it back; and he came to the city of the old prophet, to lament, and to bury him.
30 Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
And he laid his carcass in his own grave; and they made lamentation for him: 'Alas, my brother!'
31 Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
And it came to pass, after he had buried him, that he spoke to his sons, saying: 'When I am dead, then bury me in the sepulchre wherein the man of God is buried; lay my bones beside his bones.
32 Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
For the saying which he cried by the word of the LORD against the altar in Beth-el, and against all the houses of the high places which are in the cities of Samaria, shall surely come to pass.'
33 Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
After this thing Jeroboam returned not from his evil way, but made again from among all the people priests of the high places; whosoever would, he consecrated him, that he might be one of the priests of the high places.
34 Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.
And by this thing there was sin unto the house of Jeroboam, even to cut it off, and to destroy it from off the face of the earth.

< 1 Sarakuna 13 >