< 1 Tarihi 24 >

1 Waɗannan su ne sassan’ya’yan Haruna maza.’Ya’yan Haruna maza su ne Nadab, Abihu, Eleyazar da Itamar.
These were the divisions of the sons of Aaron. The sons of Aaron: Nadab, Abihu, Eleazar, and Ithamar.
2 Amma Nadab da Abihu sun mutu kafin mahaifinsu, ba su kuma haifi’ya’ya maza ba; saboda haka Eleyazar da Itamar suka yi hidimar firistoci.
But Nadab and Abihu died before their father, and had no children; therefore Eleazar and Ithamar served as priests.
3 Tare da taimakon Zadok zuriyar Eleyazar da Ahimelek wani zuriyar Itamar. Dawuda ya karkasa su zuwa ɓangarori don aikinsu bisa ga hidima.
David, with Zadok of the sons of Eleazar and Ahimelech of the sons of Ithamar, divided them according to their ordering in their service.
4 Akwai ɗumbun shugabanni a cikin zuriyar Eleyazar fiye da zuriyar Itamar, aka kuma karkasa su haka, kawuna goma sha shida daga zuriyar Eleyazar da kuma kawuna iyalai takwas daga zuriyar Itamar.
There were more chief men found of the sons of Eleazar than of the sons of Ithamar; and they were divided like this: of the sons of Eleazar there were sixteen, heads of fathers’ houses; and of the sons of Ithamar, according to their fathers’ houses, eight.
5 Aka karkasa su babu sonkai ta wurin jifa ƙuri’a, gama akwai manyan ma’aikatan wuri mai tsarki da manyan ma’aikatan Allah a cikin zuriyar Eleyazar da Itamar.
Thus they were divided impartially by drawing lots; for there were princes of the sanctuary and princes of God, both of the sons of Eleazar, and of the sons of Ithamar.
6 Shemahiya ɗan Netanel, wani Balawe ne marubuci, ya rubuta sunayensu a gaban sarki da kuma a gaban manyan ma’aikata. Zadok firist, Ahimelek ɗan Abiyatar da kuma kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa, iyali guda daga Eleyazar, guda kuma daga Itamar.
Shemaiah the son of Nethanel the scribe, who was of the Levites, wrote them in the presence of the king, the princes, Zadok the priest, Ahimelech the son of Abiathar, and the heads of the fathers’ households of the priests and of the Levites; one fathers’ house being taken for Eleazar, and one taken for Ithamar.
7 Ƙuri’a ta farko ta faɗa a kan Yehoyarib, na biyu a kan Yedahiya,
Now the first lot came out to Jehoiarib, the second to Jedaiah,
8 na uku a kan Harim, na huɗu a kan Seyorim,
the third to Harim, the fourth to Seorim,
9 na biyar a kan Malkiya, na shida a kan Miyamin,
the fifth to Malchijah, the sixth to Mijamin,
10 na bakwai a kan Hakkoz, na takwas a kan Abiya,
the seventh to Hakkoz, the eighth to Abijah,
11 na tara a kan Yeshuwa, na goma a kan Shekaniya,
the ninth to Jeshua, the tenth to Shecaniah,
12 na goma sha ɗaya a kan Eliyashib, na goma sha biyu a kan Yakim,
the eleventh to Eliashib, the twelfth to Jakim,
13 na goma sha uku a kan Huffa, na goma sha huɗu a kan Yeshebeyab,
the thirteenth to Huppah, the fourteenth to Jeshebeab,
14 na goma sha biyar a kan Bilga, na goma sha shida a kan Immer,
the fifteenth to Bilgah, the sixteenth to Immer,
15 na goma sha shida a kan Hezir, na goma sha takwas a kan Haffizzez,
the seventeenth to Hezir, the eighteenth to Happizzez,
16 na goma sha tara a kan Fetahahiya, na ashirin a kan Ezekiyel,
the nineteenth to Pethahiah, the twentieth to Jehezkel,
17 na ashirin da ɗaya wa Yakin, na ashirin da biyu a kan Gamul,
the twenty-first to Jachin, the twenty-second to Gamul,
18 na ashirin da uku wa Delahiya da kuma na ashirin da huɗu a kan Ma’aziya.
the twenty-third to Delaiah, and the twenty-fourth to Maaziah.
19 Ga tsarin aikinsu na hidima sa’ad da suka shiga haikalin Ubangiji, bisa ga ƙa’idar da kakansu Haruna ya kafa, yadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce shi.
This was their ordering in their service, to come into Yahweh’s house according to the ordinance given to them by Aaron their father, as Yahweh, the God of Israel, had commanded him.
20 Game da sauran zuriyar Lawi kuwa, Daga’ya’yan Amram maza. Shubayel; daga’ya’yan Shubayel maza. Yedehiya.
Of the rest of the sons of Levi: of the sons of Amram, Shubael; of the sons of Shubael, Jehdeiah.
21 Game da Rehabiya kuwa, daga’ya’yansa maza. Isshiya shi ne na fari.
Of Rehabiah: of the sons of Rehabiah, Isshiah the chief.
22 Daga mutanen Izhar, Shelomot; daga’ya’yan Shelomot maza, Yahat.
Of the Izharites, Shelomoth; of the sons of Shelomoth, Jahath.
23 ’Ya’yan Hebron maza su ne, Yeriya na fari, Amariya na biyu, Yahaziyel na uku da Yekameyam na huɗu.
The sons of Hebron: Jeriah, Amariah the second, Jahaziel the third, and Jekameam the fourth.
24 Ɗan Uzziyel shi ne, Mika; daga’ya’yan Mika maza, Shamir.
The sons of Uzziel: Micah; of the sons of Micah, Shamir.
25 Ɗan’uwan Mika shi ne, Isshiya; daga’ya’yan Isshiya maza, Zakariya.
The brother of Micah: Isshiah; of the sons of Isshiah, Zechariah.
26 ’Ya’yan Merari su ne, Mali da Mushi. Ɗan Ya’aziya shi ne, Beno.
The sons of Merari: Mahli and Mushi. The son of Jaaziah: Beno.
27 ’Ya’yan Merari su ne, daga Ya’aziya, Beno, Shoham, Zakkur da Ibri.
The sons of Merari by Jaaziah: Beno, Shoham, Zaccur, and Ibri.
28 Daga Mali, Eleyazar, wanda ba shi da’ya’ya maza.
Of Mahli: Eleazar, who had no sons.
29 Daga Kish, ɗan Kish shi ne, Yerameyel.
Of Kish, the son of Kish: Jerahmeel.
30 Kuma’ya’yan Mushi maza su ne, Mali, Eder da Yerimot. Waɗannan su ne Lawiyawa bisa ga iyalansu.
The sons of Mushi: Mahli, Eder, and Jerimoth. These were the sons of the Levites after their fathers’ houses.
31 Suka kuma jifa ƙuri’a, kamar dai yadda’yan’uwansu zuriyar Haruna suka yi, a gaban Sarki Dawuda da gaban Zadok, Ahimelek, da kuma a gaban kawunan iyalan firistoci da na Lawiyawa. Aka yi da iyalan wa daidai da iyalan ƙane.
These likewise cast lots even as their brothers the sons of Aaron in the presence of David the king, Zadok, Ahimelech, and the heads of the fathers’ households of the priests and of the Levites, the fathers’ households of the chief even as those of his younger brother.

< 1 Tarihi 24 >