< 1 Tarihi 22 >

1 Sai Dawuda ya ce, “Gidan Ubangiji Allah zai kasance a nan, haka kuma bagaden hadaya ta ƙonawa don Isra’ila.”
Then David said, “This is the house of Yahweh God, and this is the altar of burnt offering for Israel.”
2 Dawuda kuwa ya umarta a tattara baƙin da suke zama a Isra’ila, daga cikinsu ya sa masu farfasa duwatsu don su shirya duwatsun da aka sassaƙa saboda ginin gidan Allah.
David gave orders to gather together the foreigners who were in the land of Israel; and he set masons to cut dressed stones to build God’s house.
3 Ya tanada ƙarfe mai yawa don ƙusoshi saboda ƙyamaren hanyoyin shiga da kuma saboda mahaɗai, da ƙarin tagulla fiye da ƙirge.
David prepared iron in abundance for the nails for the doors of the gates and for the couplings, and bronze in abundance without weight,
4 Ya kuma tanada gumaguman al’ul masu yawa fiye da ƙirge, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo su wa Dawuda da yawa.
and cedar trees without number, for the Sidonians and the people of Tyre brought cedar trees in abundance to David.
5 Dawuda ya ce, “Ɗana Solomon matashi ne kuma bai gogu ba, kuma gidan da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, sananne da kuma mai daraja a idon dukan al’ummai. Saboda haka zan yi shirye-shirye saboda shi.” Sai Dawuda ya yi ɗumbun shirye-shirye kafin mutuwarsa.
David said, “Solomon my son is young and tender, and the house that is to be built for Yahweh must be exceedingly magnificent, of fame and of glory throughout all countries. I will therefore make preparation for it.” So David prepared abundantly before his death.
6 Sa’an nan ya kira ɗansa Solomon ya umarce shi yă gina gida domin Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Then he called for Solomon his son, and commanded him to build a house for Yahweh, the God of Israel.
7 Dawuda ya ce wa Solomon, “Ɗana, na yi niyya a zuciyata in gina gida saboda Sunan Ubangiji Allahna.
David said to Solomon his son, “As for me, it was in my heart to build a house to the name of Yahweh my God.
8 Amma wannan maganar Ubangiji ta zo mini, ‘Ka zub da jini mai yawa ka kuma yi yaƙe-yaƙe masu yawa. Ba za ka gina gida domin Sunana ba, domin ka zub da jini da yawa a duniya a idona.
But Yahweh’s word came to me, saying, ‘You have shed blood abundantly and have made great wars. You shall not build a house to my name, because you have shed much blood on the earth in my sight.
9 Amma za ka haifi ɗa wanda zai zama mutumin salama da kuma hutu, zan kuma ba shi hutu daga dukan abokan gābansa a kowane gefe. Za a kira shi Solomon, zai kuma kawo wa Isra’ila salama da natsuwa a zamanin mulkinsa.
Behold, a son shall be born to you, who shall be a man of peace. I will give him rest from all his enemies all around; for his name shall be Solomon, and I will give peace and quietness to Israel in his days.
10 Shi ne wanda zai gina gida saboda Sunana. Zai zama ɗana, ni kuma zan zama mahaifinsa. Zan kafa kujerar sarautarsa a bisa Isra’ila har abada.’
He shall build a house for my name; and he will be my son, and I will be his father; and I will establish the throne of his kingdom over Israel forever.’
11 “Yanzu, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, bari kuma ka yi nasara ka kuma gina gidan Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya ce za ka yi.
Now, my son, may Yahweh be with you and prosper you, and build the house of Yahweh your God, as he has spoken concerning you.
12 Bari Ubangiji ya ba ka basira da fahimi sa’ad da ya sa ka shugaba a bisa Isra’ila, saboda ka kiyaye dokar Ubangiji Allahnka.
May Yahweh give you discretion and understanding, and put you in charge of Israel, so that you may keep the law of Yahweh your God.
13 Ta haka za ka yi nasara in ka mai da hankali ga kiyaye ƙa’idodi da dokokin da Ubangiji ya ba wa Musa saboda Isra’ila. Ka yi ƙarfin hali ka kuma ƙarfafa. Kada ka ji tsoro ko ka fid da zuciya.
Then you will prosper, if you observe to do the statutes and the ordinances which Yahweh gave Moses concerning Israel. Be strong and courageous. Don’t be afraid and don’t be dismayed.
14 “Na sha wahala da yawa don in yi tanadi talentin dubu ɗari na zinariya, talenti miliyon na azurfa, ɗumbun tagulla da ƙarfe da suka wuce ƙirge da katako da dutse saboda haikalin Ubangiji. Za ka iya ƙara su.
Now, behold, in my affliction I have prepared for Yahweh’s house one hundred thousand talents of gold, one million talents of silver, and bronze and iron without weight; for it is in abundance. I have also prepared timber and stone; and you may add to them.
15 Kana da ma’aikata masu yawa, masu fafarshe duwatsu, masu gini da masu aikin katako, da kuma gwanaye a kowane irin aikin
There are also workmen with you in abundance—cutters and workers of stone and timber, and all kinds of men who are skillful in every kind of work;
16 zinariya da azurfa, tagulla da ƙarfe, masu sana’a waɗanda suka wuce ƙirge. Yanzu ka fara aiki, Ubangiji kuma ya kasance tare da kai.”
of the gold, the silver, the bronze, and the iron, there is no number. Arise and be doing, and may Yahweh be with you.”
17 Sai Dawuda ya umarta dukan shugabannin Isra’ila su taimake ɗansa Solomon.
David also commanded all the princes of Israel to help Solomon his son, saying,
18 Ya ce musu, “Ba Ubangiji Allahnku yana tare da ku ba? Bai kuma ba ku hutu a kowane gefe ba? Gama ya ba da mazaunan ƙasar gare ni, ƙasar kuma ta Ubangiji ce da mutanensa.
“Isn’t Yahweh your God with you? Hasn’t he given you rest on every side? For he has delivered the inhabitants of the land into my hand; and the land is subdued before Yahweh and before his people.
19 Yanzu fa sai ku sa zuciyarku da ranku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku fara ginin wuri mai tsarki na Ubangiji Allah, don ku kawo akwatin alkawarin Ubangiji da kayayyaki masu tsarki na Allah a cikin haikalin da za a gina saboda Sunan Ubangiji.”
Now set your heart and your soul to follow Yahweh your God. Arise therefore, and build the sanctuary of Yahweh God, to bring the ark of Yahweh’s covenant and the holy vessels of God into the house that is to be built for Yahweh’s name.”

< 1 Tarihi 22 >