< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Entonces todo Israel se congregó ante David en Hebrón y dijeron: Aquí estamos, somos hueso tuyo y carne tuya.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Porque en días anteriores, cuando aún Saúl era rey, tú sacabas y devolvías a Israel, y Yavé tu ʼElohim te dijo: Tú apacentarás a mi pueblo Israel y serás el soberano de mi pueblo Israel.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Cuando los ancianos de Israel fueron ante el rey en Hebrón, David hizo un pacto delante de Yavé. Entonces ungieron a David como rey sobre Israel, según la Palabra que Yavé dio por medio de Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Entonces David fue con todo Israel a Jerusalén, la cual es Jebús. Los jebuseos vivían en aquella tierra.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Los habitantes de Jebús dijeron a David: No entrarás aquí. Pero David capturó la fortaleza de Sion, que es la Ciudad de David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
David dijo: El que primero ataque a los jebuseos será jefe y comandante. Entonces Joab, hijo de Sarvia, subió primero y fue designado comandante.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
David vivió en la fortaleza. Por esto la llamaron Ciudad de David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Edificó la ciudad alrededor, desde el terraplén hasta el muro. Joab restauró el resto de la ciudad.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
David se engrandecía cada vez más, porque Yavé de las huestes estaba con él.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Éstos son los principales valientes que respaldaron fuertemente a David. Lo ayudaron para designarlo rey de Israel, según la Palabra de Yavé.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Éste es el número de los valientes que tuvo David: Jasobeam, hijo de Hacmoni, jefe de los 30, el cual blandió su lanza contra 300, a los cuales mató de una sola vez.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Después de él estaba Eleazar, hijo de Dodo, el ahohíta. Él era uno de los tres valientes.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Éste estuvo con David en Pas-damim cuando los filisteos se reunieron allí para la batalla. Había una parcela de tierra llena de cebada. Al huir el pueblo de los filisteos,
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
él se colocó firme en medio de la parcela y la defendió. Derrotó a los filisteos y Yavé le dio una gran victoria.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Tres de los 30 principales bajaron a la roca [donde estaba] David, en la cueva de Adulam, mientras los filisteos acampaban en el valle de Refaim.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
David estaba entonces en la fortaleza y una guarnición de los filisteos estaba en Belén.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
Entonces David sintió un vivo deseo: ¡Quién me diera a beber agua del pozo de Belén, que está en la puerta!
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Entonces los tres irrumpieron en el campamento de los filisteos, sacaron agua del pozo de Belén que está junto a la puerta y se la llevaron a David. Pero David no la quiso beber, sino la derramó ante Yavé y dijo:
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
¡Lejos esté de mí, oh mi ʼElohim, hacer esto! ¿Beberé la sangre de estos hombres que con riesgo de sus vidas la trajeron? Y no quiso beberla. Aquellos tres valientes hicieron esto.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Abisai, hermano de Joab, era el principal de los 30, el cual blandió su lanza contra 300 y los mató, y tuvo renombre entre los tres.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Fue el más ilustre de los 30 y fue su jefe, pero no igualó a los tres primeros.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Benaía, hijo de Joiada, hijo de un hombre valiente de grandes hazañas, de Cabseel, venció a los hijos de Ariel de Moab. Un día de nieve, bajó y mató a un león dentro de un foso.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
También mató a un egipcio, hombre de 2,25 metros de estatura. El egipcio llevaba una lanza como un rodillo de tejedor. Pero [Benaía] bajó con un cayado, le arrebató la lanza de la mano al egipcio y lo mató con la lanza de éste.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Esto hizo Benaía, hijo de Joiada, y tuvo tanto renombre como los tres valientes.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Ciertamente fue el más distinguido de los 30, pero no igualó a los tres primeros. David lo designó jefe de su guardia personal.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Los valientes de los ejércitos eran: Asael, hermano de Joab, Elhanán, hijo de Dodo, de Belén,
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Samote el harorita, Heles el pelonita,
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, hijo de Iques tecoíta, Abiezer anatotita,
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibecai husatita, Ilai ahohíta,
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharai netofatita, Heled, hijo de Baana netofatita,
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Itai, hijo de Ribai, de Gabaa de los hijos de Benjamín, Benaía piratonita,
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Hurai de los arroyos de Gaas, Abiel el arbatita,
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmavet barhumita, Eliaba saalbonita,
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
los hijos de Hasem gizonita, Jonatán, hijo de Sagé, ararita,
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Ahiam, hijo de Sacar ararita, Elifal, hijo de Ur,
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hefer mequeratita, Ahías pelonita,
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hezro carmelita, Naarai, hijo de Ezbai,
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel, hermano de Natán, Mibhar, hijo de Hagrai,
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Selec amonita, Naharai beerotita, escudero de Joab, hijo de Sarvia,
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira el itrita, Gareb el itrita,
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Urías heteo, Zabad, hijo de Ahlai,
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, hijo de Siza rubenita, jefe de los rubenitas, y con él 30,
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanán, hijo de Maaca, Josafat mitnita,
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzías astarotita, Sama y Jehiel, hijos de Hota aroerita,
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael, hijo de Simri, y su hermano Joha tizita,
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel mahavita, Jerebai y Josavía, hijos de Elnaam, Itma moabita,
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel, Obed, Haasiel mesobaíta.

< 1 Tarihi 11 >