< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Då kom heile Israel i hop hjå David i Hebron og sagde: «Du veit me og du er same folket.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Alt longe sidan, då Saul endå var konge, var du den som førde Israel. Og til deg hev Herren din Gud, sagt: «Du skal vera ein hyrding for Israel, folket mitt, ja, du skal vera ein hovding yver mitt folk Israel.»»
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Då so alle styresmennerne i Israel kom til kongen i Hebron, gjorde David eit samband med deim der i Hebron for Herrens åsyn, og sidan salva dei David til konge yver Israel, etter Herrens ord gjenom Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Og David for med heile Israel til Jerusalem, det er Jebus; der var jebusitarne, som endå var att i landet.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Og Jebus-buarne sagde til David: «Du kjem ikkje inn her.» Men David tok like vel Sionsborgi, det er Davidsbyen.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
Og David sagde: «Den som fyrst drep ein jebusit, kven det so er, han skal verta hovding og herførar.» Og Joab, son åt Seruja, kom fyrst upp, og vart då hovding.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
Sidan sette David seg til i borgi; difor kalla dei henne Davidsbyen.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Og han bygde byen rundt umkring, frå Millo og heilt ikring, og Joab bygde upp att det andre av byen.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
Og Davids velde auka Davids velde stødt og stendigt, og Herren, allhers drott, var med honom.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Og dette er dei gjævaste kjemporne hans David, som gav honom kraftig hjelp, i lag med heile Israel, til å verta konge, til å gjeva honom kongedømet hans, etter Herrens ord um Israel.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Dette er talet på kjemporne hans David: Jasobam, son til hakmoniføraren for kjemporne; han svinga spjotet sitt yver tri hundrad, som vart drepne i ein gong.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Og etter han kom Eleazar, son åt Dodo, ahohiten; han var ein av dei tri kjemporne.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Han var med David i Pas-Dammim, då filistarane hadde kome saman til strid, og der var ein åkerlapp fullgrodd med bygg; og folket rømde for filistarane.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
Då stødte dei seg upp midt på åkerleppen og varde honom og hogg ned filistarane, og Herren gav deim soleis ein stor siger.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Ein gong for tri av dei tretti hovdingarne nedetter berget til David ved Adullams-helleren, medan ein flokk med filistar hadde lægra seg i Refa’imsdalen.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
Men David var den gongen i borgi, og ein av filistarvaktpost var då i Betlehem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
Då fekk David brått ein sterk hug og sagde: «Å um einkvan vilde gjeva meg vatn å drikka utor brunnen som er attmed porten i Betlehem!»
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Då slo dei tri seg gjenom filistarlægret og auste vatn utor brunnen ved porten i Betlehem, og tok og bar det åt David. Men David vilde ikkje drikka det, men helte det ut for Herren.
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
For han sagde: «Gud late det aldri koma i mine tankar at eg skulde gjera slikt! Skulde eg drikka blodet av desse mennerne som hev våga livet? For med livs vågnad hev dei bore det hit.» Han vilde ikkje drikka det. Dette hadde dei tri kjemporne gjort.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Absai, bror hans Joab, var føraren for dei tri; han svinga spjotet sitt yver tri hundrad, som vart drepne. Og han var namngjeten millom dei tri.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Han var ein gong til so mykje vyrd som nokon annan i dette tritalet, og han var hovdingen deira; men endå nådde han ikkje upp til dei tri fyrste.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Benaja, son hans Jojada, som var son åt ein djerv og dådrik mann frå Kabse’el, han drap dei tvo Arielarne i Moab, og det var han som steig ned i brunnen ein snøversdag og slo i hel ei løva der.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Han felte og den risestore egyptaren som var fem alner høg. Endå egyptaren hadde eit spjot i handi som liktest stor-riven i ein vev, so gjekk han imot honom, og hadde ikkje anna til verja enn staven sin. Og han rykte spjotet ut or handi på egyptaren og drap honom med hans eige spjot.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Dette hadde Benaja Jojadason gjort. Og han var namngjeten millom dei tri kjemporne.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Ja, han var meir vyrd enn nokon av dei tretti; men upp til dei tri fyrste nådde han ikkje. Og David sette honom til hovding yver livvakti si.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Dei djerve herkjemporne var desse: Asael, bror åt Joab, Elhanan, son åt Dodo, frå Betlehem.
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Sammot, haroriten. Heles, peloniten,
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, son åt Ikkes, frå Tekoa, Abiezer frå Anatot,
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
husatiten Sibbekai, ahohiten Ilai,
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharai frå Netofa, Heled, son åt Ba’ana, frå Netofa,
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Itai, son åt Ribai, frå Gibea i Benjaminsfylket, Benaja frå Piraton,
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Hurai frå Ga’asdalarne, Abiel frå Arba,
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmavet frå Baharum, Eljahba, sa’alboniten,
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
Bene-Hasem, gizoniten, Jonatan, son åt Sage, harariten,
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Ahiam, son åt Sakar, harariten, Elifal, son åt Ur,
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hefer, mekeratiten, Ahia, peloniten,
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hesro frå Karmel, Na’arai, son åt Ezbai,
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel, bror åt Natan, Mibhar, son åt Hagri,
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Selek, ammoniten, Nahrai frå Berot, våpnsvein åt Joab Serujason,
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira frå Jeter, Gareb frå Jeter,
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Uria, hetiten, Zabad, son åt Ahlai,
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, son åt Siza, rubeniten, ein hovding millom rubenitarne, og umfram honom tretti andre,
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan, son åt Ma’aka, og Josafat, mitniten,
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzzia frå Astera, Sama og Je’uel, søner åt Hotam, aroeriten,
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael, son åt Simri, og Joha, bror hans, tisiten,
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel Hammahavim og Jeribai og Josavja, søner åt Elna’am, og Jitma, moabiten,
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel, Obed og Ja’asiel Hammesobaja.

< 1 Tarihi 11 >