< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Så kom hele Israel sammen hos David i Hebron og sa: Vi er jo av samme kjød og blod som du.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Allerede for lenge siden, ennu mens Saul var konge, var det du som førte Israel ut og inn, og Herren din Gud sa til dig: Du skal vokte mitt folk Israel, og du skal være fyrste over mitt folk Israel.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Og alle Israels eldste kom til kongen i Hebron, og David gjorde en pakt med dem i Hebron for Herrens åsyn; og de salvet David til konge over Israel efter Herrens ord ved Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Så drog David og hele Israel til Jerusalem, det er Jebus; der bodde jebusittene, landets oprinnelige innbyggere.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Og innbyggerne i Jebus sa til David: Du kommer aldri inn her. Men David inntok Sions borg - det er Davids stad.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
Og David sa: Den som først slår jebusittene, skal bli høvding og fører. Og Joab, Serujas sønn, steg først op og blev høvding.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
David tok sin bolig i borgen; derfor kaltes den Davids stad.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Og han bygget byen rundt omkring, fra Millo og rundt omkring, og Joab bygget resten av byen op igjen.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
David blev større og større, og Herren, hærskarenes Gud, var med ham.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Dette er de ypperste blandt Davids helter, som sammen med hele Israel kraftig støtet ham i hans kongedømme for å gjøre ham til konge efter Herrens ord om Israel.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Dette er Davids helter, så mange de var: Jasobam, Hakmonis sønn, høvedsmann for drabantene; han svang sitt spyd over tre hundre falne på en gang.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Efter ham kom Eleasar, sønn av ahohitten Dodo; han var en av de tre helter.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Han var med David i Pas-Dammim da filistrene hadde samlet sig der til strid. Der var et jorde som var fullt av bygg, og da folket flyktet for filistrene,
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
stilte de sig midt på jordet og berget det og slo filistrene; og Herren gav dem en stor seier.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Engang drog tre av de tretti høvdinger ned efter berget til David, som var i hulen ved Adullam. Filistrenes hær lå da i leir i Refa'im dalen.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
David var dengang selv i borgen, og filistrenes forpost var i Betlehem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
Så kom det en brå lyst over David, og han sa: Hvem lar mig få vann å drikke av den brønn som er ved porten i Betlehem?
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Da brøt de tre sig igjennem filistrenes leir og øste vann op av brønnen ved Betlehems port og tok det med sig og kom til David med det; men David vilde ikke drikke det - han øste det ut for Herren.
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
Og han sa: Min Gud, la det være langt fra mig å gjøre dette! Skulde jeg drikke disse menns blod, som har satt sitt liv i fare? For med fare for sitt liv har de båret det hit. Og han vilde ikke drikke det. Dette gjorde de tre helter.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Så var det Absai, bror til Joab; han var fører for de tre. Han svang sitt spyd over tre hundre falne; og han hadde et navn blandt de tre.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Fremfor de tre var han dobbelt æret og blev deres høvding; men til de tre nådde han ikke op.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Så var det Benaja, sønn av Jojada, som var sønn av en djerv seierrik stridsmann fra Kabse'el; han slo Moabs to løvehelter. En dag det hadde snedd, steg han ned i en brønn og slo en løve ihjel.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Likeledes slo han ihjel en egypter, en mann som var fem alen lang; egypteren hadde et spyd som en veverstang i hånden; men han gikk ned mot ham med sin stav og rev spydet ut av hånden på egypteren og drepte ham med hans eget spyd.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Dette gjorde Benaja, Jojadas sønn; han hadde et navn blandt de tre helter.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Fremfor de tretti var han æret, men til de tre nådde han ikke op. David gav ham plass blandt sine fortrolige rådgivere.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
De djerveste i hæren var: Asael, bror til Joab; Elhanan, Dodos sønn, fra Betlehem;
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
haroritten Sammot; pelonitten Heles;
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
teko'itten Ira, sønn av Ikkes; anatotitten Abieser;
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
husatitten Sibbekai; ahohitten Ilai;
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
netofatitten Maharai; netofatitten Heled, sønn av Ba'ana;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Itai, Ribais sønn, fra Gibea i Benjamins stamme; piratonitten Benaja;
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Hurai fra Ga'as-dalene; arbatitten Abiel;
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
baharumitten Asmavet; sa'albonitten Eljahba;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
gisonitten Bene-Hasem; hararitten Jonatan, sønn av Sage;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
hararitten Akiam, sønn av Sakar; Elifal, sønn av Ur;
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
mekeratitten Hefer; pelonitten Akia;
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
karmelitten Hesro; Na'arai, sønn av Esbai;
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel, bror til Natan; Mibhar, sønn av Hagri;
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
ammonitten Selek; berotitten Nahrai, Joabs, Serujas sønns våbensvenn;
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
jitritten Ira; jitritten Gareb;
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
hetitten Uria; Sabad, sønn av Ahlai;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
rubenitten Adina, sønn av Sisa, overhode for rubenittene, og foruten ham tretti;
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan, sønn av Ma'aka, og mitnitten Josafat;
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
asteratitten Ussia; Sama og Je'uel, sønner av aroeritten Hotam;
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael, sønn av Simri, og hans bror Joha, tisitten;
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel Hammahavim og Jeribai og Josavja, sønner av Elna'am, og moabitten Jitma;
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel og Obed og Ja'asiel Hammesobaja.

< 1 Tarihi 11 >