< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
A LAILA akoakoa ae la ka Iseraela a pau io Davida la i Heberona, i mai la, Eia hoi, hookahi no ko kakou iwi a me ka io.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
I ka wa mamua no hoi, ia Saula i alii ai, o oe no ka mea nana i alakai aku a i alakai mai i ka Iseraela: i mai la hoi o Iehova o kou Akua ia oe, E hanai oe i ko'u poe kanaka i ka Iseraela; a e lilo oe i alii no ko'u poe kanaka no ka Iseraela.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Nolaila, i hele mai na lunakahiko a pau o ka Iseraela i ke alii ma Heberona; a hoopaa iho la o Davida i berita me lakou ma Heberona, imua o Iehova: a poni iho la lakou ia Davida i alii no ka Iseraela, e like me ka olelo a Iehova ma o Samuela la.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Hele aku la o Davida me ka Iseraela a pau i Ierusalema, oia o Iebusa. kahi i noho ai ka Iebusa, na kanaka o ia aina.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Olelo mai la na kanaka o Iebusa ia Davida, Aole oe e hele mai ia nei. Aka, lawe lilo o Davida i ka pakaua o Ziona, oia ke kulanakauhale o Davida.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
I mai la o Davida, O ka mea pepehi mua i ka Iebusi, e lilo ia i pookela a i lunakoa. A o Ioaba, o ke keiki a Zeruia i pii mua aku la, a lilo ae la ia i pookela.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
A noho iho la o Davida ma ka pakaua; nolaila, kapa aku la lakou ia wahi, O ke kulanakauhale o Davida.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Kukulu iho la ia i ke kulanakauhale a puni, mai Milo aku a puni: a kukulu hou iho la o Ioaba i na wahi i koe o ke kulanakauhale.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
Mahuahua ae la o Davida a nui loa: no ka mea, me ia pu o Iehova sabaota.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Eia hoi na pookela o na kanaka ikaika ia Davida, ka poe i hooikaika pu me ia iloko o kona aupuni a me ka Iseraela a pau, e hooalii ia ia, e like me ka olelo a Iehova no ka Iseraela.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Eia ka helu ana o na kanaka ikaika ia Davida: o Iasobeama ka Hakemoni, ke pookela o na lunakoa: hoaka ae la ia i kana ihe e ku e i na haneri kanaka ekolu, a make lakou i ka manawa hookahi.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Mahope iho ona o Eleazara ke keiki a Dodo ka Ahohi, kekahi o na kanaka ikaika loa ekolu.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Aia no ia me Davida ma Padamima, ilaila i akoakoa ai ko Pilisetia i ke kaua, i kahi i paa pu ai ka honua i ka bale: a naholo aku la na kanaka imua o ko pilisetia.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
A ku iho la lakou iwaena konu o ua aina la, a hoomalu iho la ia wahi, a pepehi iho la i ko Pilisetia; a hoola ae la o Iehova ia lakou i ke ola nui.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Iho aku la na mea ekolu o ka poe luna he kanakolu i kahi paa io Davida la iloko o ke ana o Adulama: a hoomoana iho la ka poe kauwa o Pilisetia ma ke awawa i Repaima.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
Haila o Davida iloko o kahi paa, a ma Betolehema ka pakaua o ko Pilisetia ia manawa.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
Makewai iho la o Davida, i mai la, Nani ino kuu makemake e haawi mai kekahi i wai e inu no ka luawai mai o Betelehema, aia ma ka ipuka!
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Wahi ae la aa mau kanaka ekolu la i ka poe kaua o ko Pilisetia, a huki mai la i ka wai, mailoko o ka luawai o Betelehema ma ka ipuka, lalau aku la, a lawe mai la io Davida la: aka, aole o Davida i manao e inu ia mea, a ninini aku no ia mea no Iehova.
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
I aku la ia, E papa mai ko'u Akua ia'u. i ole au e hana ia mea: e inu no auei au i ke koko o keia mau kanaka, me ko lakou ola? no ka mea, me ke ola wale no lakou i lawe mai nei ia mea: nolaila, aole ia i make inu. Pela i hana'i ia mau kanaka ikaika loa ekolu.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
A o Abisai ke kaikaina o Ioaba, oia ke pookela o na mea ekolu: no ka mea, hoaka ae la ia i kona ihe e ku e i na kanaka ekolu haneri, a pepehi iho la ia ia lakou, a loaa ia ia ka inoa iwaena o ua mau kanaka ikaika la ekolu.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
No na mea ekolu, ua oi aku kona koikoi imua o na mea elua, nolaila, oia ko laua luna: aka, aole i hiki aku kona e like me ko kela poe ekolu.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
O Benaia ke keiki a Iehoiada, ke keiki a kekahi kanaka ikaika no Kabezeela, he nui kana hana kupanaha: pepehi iho la ia i elua kanaka ikaika loa o Moaba: iho iho la hoi ia iloko o ka lua, a pepehi iho la i ka liona i ka la e haule ana ka hau.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Pepehi iho la hoi oia i kekahi kanaka Aigupita, he kanaka nunui, he elima hailima ke kiekie: a he ihe no ma ka lima o ka Aigupita, e like me ka laau o ka mea ulana lole: a iho aku la kela io na la me ke kookoo, a kaili ae la i ka ihe mailoko ae o ka lima o ka Aigupita, a pepehi iho la ia ia me kana ihe.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
O na mea keia a Benaia a ke keiki a Iehoiada i hana'i, a loaa ia ia ka inoa iwaena o ka poe kanaka ikaika ekolu.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Aia hoi, he koikoi no ia iwaena o ke kanakolu, aole hoi i hiki aku kona i ko kela poe ekolu. A hoonoho aku la o Davida ia ia i kuhina nona.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Eia hoi na kanaka koa o na kaua: o Asahela ke kaikaina o loaba, o Elehanana ke keiki a Dodo no Betelehema,
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
O Samota no Harora, o Heleza no Pelona.
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
O Ira ke keiki a Ikesa no Tekoa, o Abiezera no Anetota,
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
O Sibekai no Husata, o Hai no Ahota.
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
O Maharai no Netopa, o Heleda ke keiki a Baana no Netopa,
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
O Itai ke keiki a Ribai no Gibea, no na mamo a Beniamina, o Benaia no Piratona,
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
O Hurai no na awawa o Gaasa, o Abiela, no Arabata,
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
O Azemaveta no Baharuma, o Eliaba no Saalebo,
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
O na keiki a Hasema no Gilo, o Ionatana ke keiki a Sage no Harara.
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
O Ahiama ke keiki a Sakara no Harara, o Elipala ke keiki a Ura,
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
O Hepera no Mekerata, o Ahiia no Pelona,
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
O Hezero no Karemela, o Naarai ke keiki a Ezebai,
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
O Ioela ka hoahanau o Natana, o Mibehara ke keiki a Hageri,
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
O Zeleka ka Amona, o Naharai no Berota, ka mea lawe i na mea kaua a Ioaba ke keiki a Zeruia,
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
O Ira no Itera, o Gareba no Itera,
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
O Auria ka Heta, o Zabada ke keiki a Ahelai,
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
O Adina ke keiki a Siza a ka Reubena, he luna ia o ka Reubena, a he kanakolu no me ia,
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
O Hanana ke keiki a Maaka, o Iosapata no Mitana,
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
O Uzia no Aseterata, o Sama, a o Iehiela, na keiki a Hotana no Aroera,
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
O Idiaela ke keiki a Simeri, a o Ioha kona kaikaina, no Tiza,
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
O Eliela no Mahava, o Ieribai, a o Iosavia, na keiki a Elenaama, o Itema ka Moaba,
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
O Eliela, o Obeda, a o Iasiela ka Mesoba.

< 1 Tarihi 11 >