< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Et tous les Israélites formèrent assemblée auprès de David à Hébron et dirent: Voici, nous sommes tes os et ta chair.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Déjà hier et avant-hier, déjà pendant le règne de Saül, c'était toi qui menais en campagne et ramenais Israël, et l'Éternel, ton Dieu, t'a dit: C'est toi qui seras le pasteur de mon peuple d'Israël, et c'est toi qui seras prince de mon peuple d'Israël.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Ainsi se présentèrent tous les Anciens d'Israël au Roi en Hébron et David solennisa un pacte avec eux à Hébron devant l'Éternel; et ils oignirent David roi d'Israël aux termes de la parole de l'Éternel prononcée par l'organe de Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Et David et tous les Israélites se portèrent sur Jérusalem, c'est- à-dire Jébus; or là vivaient les Jébusites habitants du pays.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Et les habitants de Jébus dirent à David: Tu n'entreras pas ici. Mais David s'empara de la citadelle de Sion, c'est-à-dire, de la Cité de David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
Et David dit: Le premier qui battra les Jébusites aura rang de chef et de général. Et le premier qui escalada fut Joab, fils de Tseruïa, et il devint chef.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
Et David habita la citadelle; c'est pourquoi elle reçut le nom de Cité de David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Et il éleva la cité dans son pourtour, à partir de Millo, et l'enceinte entière, et Joab restaura le restant de la ville.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
Et David allait toujours grandissant et l'Éternel des armées était avec lui.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Suivent les principaux héros qu'avait David, qui lui prêtèrent main forte lors de son avènement, avec tout Israël, pour le faire roi selon la parole de l'Éternel concernant Israël.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Et voici la liste des héros qu'avait David: Jasobeam, fils de Hachmoni, chef des trente, il brandissait sa lance sur trois cents hommes tués tout d'une haleine.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Et après lui Eléazar, fils de Dodo, l'Ahohite; il était l'un des trois héros.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
C'est lui qui était avec David à Pas-Damim, lorsque les Philistins s'étaient concentrés là pour le combat. Et il y avait là une pièce de terre, pleine d'orge, et la troupe s'enfuit devant les Philistins;
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
alors ils se postèrent au milieu du champ et le délivrèrent et battirent les Philistins, et l'Éternel accorda une grande victoire.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Et ces trois qui faisaient partie des trente chefs, descendirent au rocher vers David dans la grotte d'Adullam, et le camp des Philistins était assis dans la vallée de Rephaïm.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
Or David se trouvait à ce moment sur la hauteur, et il y avait alors à Bethléhem un poste de Philistins.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
Et David fit un souhait et dit: Qui me fera boire de l'eau de la citerne de Bethléhem, qui est dans la porte?
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Alors les trois se firent jour à travers le campement des Philistins, et puisèrent de l'eau à la citerne de Bethléhem dans la porte, et ils l'apportèrent et l'offrirent à David; mais David ne voulut pas la boire et il la répandit en hommage à l'Éternel
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
et dit: Mon Dieu me préserve de faire pareille chose! Boirais-je le sang de ces hommes qui ont risqué leur vie? Car c'est au péril de leur vie qu'ils l'ont apportée. Il ne voulut donc pas la boire. Tel est l'exploit des trois héros.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Et Abisaï, frère de Joab: il était le chef des Trois, et il brandit sa lance sur trois cents tués et il avait un nom dans les Trois.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Il était honoré par les Trois de la seconde série, et était leur chef, mais il n'atteignait pas aux Trois [premiers].
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Benaïa, fils de Joiada, fils d'un brave, illustre par ses exploits, du Cabtséel; c'est lui qui abattit les deux Ariels de Moab. C'est aussi lui qui descendit et abattit le lion dans la citerne un jour de neige.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
C'est aussi lui qui terrassa l'homme d'Egypte, un homme ayant une stature de cinq coudées, et dans la main de l'Égyptien était une lance comme l'ensuble d'un tisserand, et il fondit sur lui avec le bâton, et arracha la lance de la main de l'Égyptien, qu'il tua avec sa lance.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Tels sont les faits de Benaïa, fils de Joiada, et il avait avec un nom entre les Trois héros.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Voici, il était honoré par les trente, mais il n'atteignait pas aux trois premiers. Et David le mit à la tête de sa garde du corps.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Et les chefs des ces corps d'armée étaient: Asahel, frère de Joab; Elchanam fils de Dodo, de Bethléhem;
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Sammoth l'Harorite; Hélets, le Pelonite;
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, fils de Ickesch de Thékôa; Abiézer, d'Anatoth;
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibchaï le Husathite; Ilaï l'Ahohite;
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maheraï de Nétophah; de Héled, fils de Baëna, de Nétophah;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Ithaï, fils de Ribaï, de Gibea des Benjaminites; Benaïa, de Piratheon;
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Huraï de Nahalei-Gaas; Abiel de Arba;
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmaveth, le Baherumite; Elihaba, de Saalbon;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
Benei-Hasem, de Gizon; Jonathan, fils de Sagè, de Harar;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Hahiam, fils de Sachar, de Harar; Eliphal, fils de Hur;
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hépher, de Mechébaï; Ahia, le Pelonite;
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hetsro, le Carmélite; Naaraï, fils de Ezbaï;
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joël, frère de Nathan; Mibehar, fils de Hagri;
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Tsélec, l'Ammonite; Naheraï, le Bérothite, écuyer de Joab, fils de Tseruïa;
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Irah, de Jéther; Gareb, de Jéther;
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Uria le Héthien; Zabad, fils de Ahelaï;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, fils de Siza, le Rubénite, chef des Rubénites, suivi de trente hommes;
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan, fils de Maëcha, et Josaphat, le Mithenite;
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzzia d'Astherah; Sama et Jehiel, fils de Hotham d'Aroër;
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael, fils de Simri, et Joha, son frère, le Thitsite;
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel de Mahevim; Jeribaï et Josavia, fils d'Elnaam; et Jithma, le Moabite;
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel et Obed et Jaësiel-Hammetsobaïa.

< 1 Tarihi 11 >