< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Alors tout Israël se rassembla auprès de David à Hébron, en disant: « Voici, nous sommes tes os et ta chair.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Autrefois, même lorsque Saül était roi, c'est toi qui as fait sortir et entrer Israël. Yahvé ton Dieu t'a dit: « Tu seras le berger de mon peuple d'Israël, et tu seras le prince de mon peuple d'Israël. »
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Et tous les anciens d'Israël vinrent auprès du roi à Hébron, et David fit alliance avec eux à Hébron, devant Yahvé. Ils oignirent David comme roi d'Israël, selon la parole de Yahvé par Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
David et tout Israël allèrent à Jérusalem (appelée aussi Jébus); les Jébusiens, habitants du pays, étaient là.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Les habitants de Jébus dirent à David: « Tu n'entreras pas ici! » Néanmoins, David prit la forteresse de Sion. C'est la ville de David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
David avait dit: « Celui qui frappera le premier les Jébusiens sera chef et capitaine. » Joab, fils de Tseruja, monta le premier, et fut nommé chef.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
David habitait dans la forteresse; c'est pourquoi on l'appelait la ville de David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Il construisit la ville tout autour, depuis Millo jusqu'aux environs; et Joab répara le reste de la ville.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
David devenait de plus en plus grand, car l'Éternel des armées était avec lui.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Et voici les chefs des hommes forts que David avait, qui se sont montrés forts avec lui dans son royaume, avec tout Israël, pour le faire roi, selon la parole de l'Éternel sur Israël.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
Voici le nombre des vaillants hommes que David avait: Jashobeam, fils d'un Hachmonite, chef des trente; il leva sa lance contre trois cents personnes et les tua en une seule fois.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Après lui, Éléazar, fils de Dodo, l'Ahochite, qui était l'un des trois hommes forts.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Il était avec David à Pasdammim, et là, les Philistins étaient rassemblés pour combattre, là où il y avait un terrain plein d'orge; et le peuple fuyait devant les Philistins.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
Ils se placèrent au milieu du champ, le défendirent et tuèrent les Philistins, et Yahvé les sauva par une grande victoire.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Trois des trente chefs descendirent au rocher vers David, dans la grotte d'Adullam; et l'armée des Philistins campait dans la vallée des Rephaïm.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
David était alors dans la forteresse, et la garnison des Philistins était en ce moment à Bethléem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
David se languissait et disait: « Oh, si quelqu'un me donnait à boire de l'eau du puits de Bethléem, qui est près de la porte! ».
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Les trois hommes traversèrent l'armée des Philistins, puisèrent de l'eau dans le puits de Bethléem, près de la porte, la prirent et l'apportèrent à David. David ne voulut pas en boire, mais il la versa à Yahvé,
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
et dit: « Mon Dieu me défend de faire cela! Boirais-je le sang de ces hommes qui ont mis leur vie en péril? ». Car ils avaient risqué leur vie pour l'apporter. Il n'a donc pas voulu le boire. Les trois hommes forts firent ces choses.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Abishaï, frère de Joab, était le chef des trois, car il leva sa lance contre trois cents personnes et les tua, et il eut un nom parmi les trois.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Parmi les trois, il était plus honorable que les deux autres, et il fut fait leur chef; cependant il n'était pas compris dans les trois.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Benaja, fils de Jehoiada, fils d'un homme vaillant de Kabzeel, qui avait fait des exploits, tua les deux fils d'Ariel de Moab. Il descendit aussi et tua un lion au milieu d'une fosse, un jour de neige.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Il tua un Égyptien, un homme de haute stature, haut de cinq coudées. Il descendit vers lui avec un bâton, arracha la lance de la main de l'Égyptien et le tua avec sa propre lance.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Benaja, fils de Jehojada, fit ces choses et eut un nom parmi les trois vaillants hommes.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Voici, il était plus honorable que les trente, mais il n'atteignait pas les trois, et David le plaça à la tête de sa garde.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Parmi les vaillants soldats, il y avait aussi Asaël, frère de Joab, Elhanan, fils de Dodo, de Bethléhem,
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Schammoth, de Haror, Hélez, de Pelon,
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, fils d'Ikkesh, de Teko, Abiézer, d'Anathoth,
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibbecaï, de Huschath, Ilaï, d'Ahoh,
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharaï, de Netophath, Héled, fils de Baana, de Netophath,
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Ithaï, fils de Ribaï, de Guibea, des fils de Benjamin, Benaja, le Pirathonien,
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Huraï, des ruisseaux de Gaash, Abiel, l'Arbathien,
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmaveth, le Baharumite, Eliahba, le Shaalbonite,
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
les fils de Hachem, le Gizonite, Jonathan, fils de Schagee, le Hararien,
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Ahiam, fils de Sacar, le Hararien, Eliphal, fils d'Ur,
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hépher, le Méchathien, Achija, le Pélonite,
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hezro, le Carmélite, Naaraï, fils d'Ezbaï,
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joël, frère de Nathan, Mibhar, fils de Hagri,
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Zelek, l'Ammonite, Naharaï, le Berothite, porteur d'armes de Joab, fils de Tseruja,
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira, l'Ithrite, Gareb, l'Ithrite,
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Urie, le Hittite, Zabad, fils d'Ahlaï,
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, fils de Schiza, le Rubénite, chef des Rubénites, et trente avec lui,
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan, fils de Maaca, Josaphat, le Mithnite,
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzzia, l'Asterathite, Shama et Jeiel, fils d'Hotham, l'Aroérite,
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediaël, fils de Shimri, et Joha, son frère, le Tizite,
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Éliel, le Mahavite, Jeribaï, et Joschavia, fils d'Elnaam, et Ithma, le Moabite,
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Éliel, Obed, et Jaasiel, le Mézobaite.

< 1 Tarihi 11 >