< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Then all Israel came to David at Hebron and said, “Look, we are your flesh and bone.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
In the recent past, when Saul was king over us, it was you who led the Israelite army. Yahweh your God said to you, 'You will shepherd my people Israel, and you will become a ruler over my people Israel.'”
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
So all the elders of Israel came to the king at Hebron, and David made a covenant with them before Yahweh. They anointed David king over Israel. In this way, the word of Yahweh that had been declared by Samuel came true.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
David and all Israel went to Jerusalem (that is, Jebus). Now the Jebusites, the inhabitants of the land, were there.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
The inhabitants of Jebus said to David, “You will not come in here.” But David took the stronghold of Zion, that is, the city of David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
David had said, “Whoever attacks the Jebusites first will become chief and commander.” So Joab son of Zeruiah attacked first, so he was made the chief.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
Then David began to live in the stronghold. So they called it the city of David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
He built the city all around from the Millo and back to the surrounding wall. Joab restored the rest of the city.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
David became greater and greater because Yahweh of hosts was with him.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
These were the leaders David had, who showed themselves strong with him in his kingdom, together with all Israel, to make him king, obeying the word of Yahweh concerning Israel.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
This is a list of David's mighty men: Jashobeam, the son of a Hachmonite, was commander of the officers. He killed three hundred men with his spear on one occasion.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
After him was Eleazar son of Dodo, the Ahohite, who was one of the three mighty men.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
He was with David at Pas Dammim, and there the Philistines assembled together for battle, where there was a barley field and the army fled from the Philistines.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
They stood in the middle of the field. They defended it and cut down the Philistines and Yahweh rescued them with a great victory.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Then three of the thirty leaders went down to the rock to David, to the cave of Adullam. The army of the Philistines was camped in the Valley of Rephaim.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
At that time David was in his stronghold, a cave, while the Philistines had established their camp at Bethlehem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
David was longing for water and said, “If only someone would give me water to drink from the well at Bethlehem, the well that is by the gate!”
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
So these three mighty men broke through the army of the Philistines and drew water out of the well of Bethlehem, the well at the gate. They took the water and brought it to David, but he refused to drink it. Instead, he poured it out to Yahweh.
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
Then he said, “May it be that I should never do this! Should I drink the blood of these men who have risked their lives?” Because they had put their lives at risk, David refused to drink it. These were the deeds of the three mighty men.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Abishai brother of Joab was captain over the Three. He once used his spear against three hundred and killed them. He is mentioned along with the Three.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Of the Three, he was given double honor and became their captain, even though he was not one of them.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Benaiah son of Jehoiada was a brave warrior from Kabzeel, who did great deeds. He killed the two sons of Ariel of Moab. He also went down into a pit and killed a lion on a day when the snow was falling.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
He even killed an Egyptian, a man five cubits tall. The Egyptian had a spear like a weaver's beam, but he went down to him with only a staff. He seized the spear out of the Egyptian's hand and killed him with his own spear.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
Benaiah son of Jehoiada did these feats, and he was named alongside the three mighty men.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
He was more highly regarded than the thirty soldiers in general, but he was not regarded quite as highly as the three mighty men. Yet David put him in charge of his bodyguard.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
The mighty men were Asahel brother of Joab, Elhanan son of Dodo of Bethlehem,
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Shammoth the Harorite, Helez the Pelonite,
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira son of Ikkesh the Tekoite, Abiezer the Anathothite,
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibbekai the Hushathite, Ilai the Ahohite,
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharai the Netophathite, Heled son of Baanah the Netophathite,
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Ithai son of Ribai of Gibeah of Benjamin's descendants, Benaiah the Pirathonite,
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Hurai of the valleys of Gaash, Abiel the Arbathite,
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmaveth the Baharumite, Eliahba the Shaalbonite,
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
the sons of Hashem the Gizonite, Jonathan son of Shagee the Hararite,
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Ahiam son of Sakar the Hararite, Eliphal son of Ur,
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hepher the Mekerathite, Ahijah the Pelonite,
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hezro the Carmelite, Naarai son of Ezbai,
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel brother of Nathan, Mibhar son of Hagri,
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Zelek the Ammonite, Naharai the Berothite (the armor bearer of Joab son of Zeruiah),
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira the Ithrite, Gareb the Ithrite,
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Uriah the Hittite, Zabad son of Ahlai,
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina son of Shiza the Reubenite (a chief of the Reubenites) and thirty with him,
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan son of Maacah, and Joshaphat the Mithnite,
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzzia the Ashterathite, Shama and Jeiel sons of Hotham the Aroerite,
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael son of Shimri, Joha (his brother the Tizite),
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel the Mahavite, Jeribai and Joshaviah sons of Elnaam, Ithmah the Moabite,
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel, Obed, and Jaasiel the Mezobaite.

< 1 Tarihi 11 >