< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Then all Israel gathered themselves to David unto Hebron, saying: 'Behold, we are thy bone and thy flesh.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
In times past, even when Saul was king, it was thou that didst lead out and bring in Israel; and the LORD thy God said unto thee: Thou shalt feed My people Israel, and thou shalt be prince over My people Israel.'
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
So all the elders of Israel came to the king to Hebron; and David made a covenant with them in Hebron before the LORD; and they anointed David king over Israel, according to the word of the LORD by the hand of Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
And David and all Israel went to Jerusalem — the same is Jebus — and the Jebusites, the inhabitants of the land, were there.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
And the inhabitants of Jebus said to David: 'Thou shalt not come in hither.' Nevertheless David took the stronghold of Zion; the same is the city of David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
And David said: 'Whosoever smiteth the Jebusites first shall be chief and captain.' And Joab the son of Zeruiah went up first, and was made chief.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
And David dwelt in the stronghold; therefore they called it the city of David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
And he built the city round about, from Millo even round about; and Joab repaired the rest of the city.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
And David waxed greater and greater; for the LORD of hosts was with him.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
Now these are the chief of the mighty men whom David had, who held strongly with him in his kingdom, together with all Israel, to make him king, according to the word of the LORD concerning Israel.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
And this is the number of the mighty men whom David had: Jashobeam, the son of a Hachmonite, the chief of the captains; he lifted up his spear against three hundred and slew them at one time.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
And after him was Eleazar the son of Dodo, the Ahohite, who was one of the three mighty men.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
He was with David at Pas-dammim, and there the Philistines were gathered together to battle, where was a plot of ground full of barley; and the people fled from before the Philistines.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
But they stood in the midst of the plot, and defended it, and slew the Philistines; and the LORD saved them by a great victory.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
And three of the thirty chiefs went down to the rock to David, unto the cave of Adullam; and the host of the Philistines were encamped in the valley of Rephaim.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
And David was then in the stronghold, and the garrison of the Philistines was then in Beth-lehem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
And David longed, and said: 'Oh that one would give me water to drink of the well of Beth-lehem, which is by the gate!'
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
And the three broke through the host of the Philistines, and drew water out of the well of Beth-lehem, that was by the gate, and took it, and brought it to David; but David would not drink thereof, but poured it out unto the LORD,
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
and said: 'My God forbid it me, that I should do this; shall I drink the blood of these men that have put their lives in jeopardy? for with the jeopardy of their lives they brought it.' Therefore he would not drink it. These things did the three mighty men.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
And Abishai, the brother of Joab, he was chief of the three; for he lifted up his spear against three hundred and slew them, and had a name among the three.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Of the three in the second rank he was the most honourable, and was made their captain; howbeit he attained not to the first three.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Beniah the son of Jehoiada, the son of a valiant man of Kabzeel, who had done mighty deeds, he smote the two altar-hearths of Moab; he went down also and slew a lion in the midst of a pit in time of snow.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
And he slew an Egyptian, a man of great stature, five cubits high; and in the Egyptian's hand was a spear like a weaver's beam; and he went down to him with a staff, and plucked the spear out of the Egyptian's hand, and slew him with his own spear.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
These things did Benaiah the son of Jehoiada, and had a name among the three mighty men.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Behold, he was more honourable than the thirty, but he attained not to the first three; and David set him over his guard.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Also the mighty men of valour: Asahel the brother of Joab, Elhanan the son of Dodo of Beth-lehem;
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Shammoth the Harorite, Helez the Pelonite;
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira the son of Ikkesh the Tekoite, Abiezer the Anathothite;
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibbecai the Hushathite, Ilai the Ahohite;
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Mahrai the Netophathite, Heled the son of Baanah the Netophathite;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Ithai the son of Ribai of Gibeah of the children of Benjamin, Benaiah the Pirathonite;
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Hurai of Nahale-gaash, Abiel the Arbathite;
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Azmaveth the Baharumite, Eliahba the Shaalbonite;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
the sons of Hashem the Gizonite, Jonathan the son of Shageh the Hararite;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Ahiam the son of Sacar the Hararite, Eliphal the son of Ur;
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hepher the Mecherathite, Ahijah the Pelonite;
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hezro the Carmelite, Naarai the son of Ezbai;
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel the brother of Nathan, Mibhar the son of Hagri;
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Zelek the Ammonite, Nahrai the Berothite, the armour-bearer of Joab the son of Zeruiah;
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira the Ithrite, Gareb the Ithrite;
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Uriah the Hittite, Zabad the son of Ahlai;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina the son of Shiza the Reubenite, a chief of the Reubenites, and thirty with him;
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan the son of Maacah, and Joshaphat the Mithnite;
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzzia the Ashterathite, Shama and Jeiel the sons of Hotham the Aroerite;
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael the son of Shimri, and Joha his brother, the Tizite;
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel the Mahavite, and Jeribai, and Joshaviah, the sons of Elnaam, and Ithmah the Moabite;
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel, and Obed, and Jaasiel the Mezobaite.

< 1 Tarihi 11 >