< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Then all of Israel was gathered to David at Hebron, saying: “We are your bone and your flesh.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Also, yesterday and the day before, when Saul still reigned, you were the one who led out and brought in Israel. For the Lord your God said to you: ‘You shall pasture my people Israel, and you shall be the leader over them.’”
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Therefore, all those greater by birth of Israel went to the king at Hebron. And David formed a pact with them before the Lord. And they anointed him king over Israel, in accord with the word of the Lord, which he spoke by the hand of Samuel.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Then David and all of Israel went to Jerusalem. The same is Jebus, where the Jebusites, the inhabitants of the land, were.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
And those who were living in Jebus said to David: “You shall not enter here.” But David seized the stronghold of Zion, which is the city of David.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
And he said, “Whoever shall strike the Jebusites first, shall be ruler and commander.” And so Joab, the son of Zeruiah, ascended first, and he was made the leader.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
Then David lived in the stronghold, and for this reason it was called the City of David.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
And he built up the city all around, from Millo even to every side. But Joab built the rest of the city.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
And David continued advancing and increasing, and the Lord of hosts was with him.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
These are the leaders of the strong men of David, who assisted him, so that he would become king over all of Israel, in accord with the word of the Lord, which he spoke to Israel.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
And this is the number of the robust of David: Jashobeam, the son of a Hachmonite, leader among the thirty. He lifted up his spear over three hundred, who were wounded at one time.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
And after him, there was Eleazar, the son of his uncle, an Ahohite, who was among the three powerful ones.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
He was with David in Pasdammim, when the Philistines were gathered to that place for battle. Now the field of that region was full of barley, but the people had fled from the face of the Philistines.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
These men stood in the midst of the field, and they defended it. And when they had struck down the Philistines, the Lord gave a great salvation to his people.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Then three from the thirty leaders descended to the rock where David was, to the cave of Adullam, when the Philistines had made camp in the Valley of the Rephaim.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
Now David was in a stronghold, and a garrison of the Philistines was in Bethlehem.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
And then David desired and said, “O if only someone would give me water from the well of Bethlehem, which is at the gate!”
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Therefore, these three broke through to the midst of the camp of the Philistines, and they drew water from the well of Bethlehem, which was at the gate. And they took it to David, so that he might drink. But he was not willing; and instead, he offered it as a libation to the Lord,
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
saying: “Far be it from me, that I would do this in the sight of my God, and that I would drink the blood of these men. For at the peril of their own lives, they brought the water to me.” And for this reason, he was not willing to drink. The three most powerful accomplished these things.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Also, Abishai, the brother of Joab, was the leader of the three, and he lifted up his spear against three hundred, who were wounded. And he was most renowned among the three,
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
and he was famous among the second three and their leader. Yet truly, he did not reach as far as the first three.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Benaiah, the son of Jehoiada, from Kabzeel, was a very mature man, who had accomplished many deeds. He struck down the two lions of God from Moab. And he descended and killed a lion in the middle of a pit, in the time of snow.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
And he struck down an Egyptian man, whose stature was five cubits, and who had a spear like a weaver’s beam. And yet he descended to him with a staff. And he seized the spear that he was holding in his hand. And he killed him with his own spear.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
These things were done by Benaiah, the son of Jehoiada, who was most renowned among the three robust ones,
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
the first among the thirty. Yet truly, he did not reach as far as the three. Then David placed him beside his ear.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Moreover, the strongest men of the army were Asahel, the brother of Joab; and Elhanan, the son of his uncle, from Bethlehem;
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Shammoth, a Harorite; Helez, a Pelonite;
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Ira, the son of Ikkesh, a Tekoite; Abiezer, an Anathothite;
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Sibbecai, a Hushathite; Ilai, an Ahohite;
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Maharai, a Netophathite; Heled, the son of Baanah, a Netophathite;
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Ithai, the son of Ribai, from Gibeah, of the sons of Benjamin; Benaiah, a Pirathonite;
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Hurai, from the torrent Gaash; Abiel, an Arbathite; Azmaveth, a Baharumite; Eliahba, a Shaalbonite.
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
The sons of Hashem, a Gizonite: Jonathan, the son of Shagee, a Hararite;
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
Ahiam, the son of Sachar, a Hararite;
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Eliphal, the son of Ur;
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Hepher, a Mecherathite; Ahijah, a Pelonite;
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Hezro, a Carmelite; Naharai, the son of Ezbai;
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Joel, the brother of Nathan; Mibhar, the son of Hagri;
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Zelek, an Ammonite; Naarai, a Beerothite, the armor bearer of Joab, the son of Zeruiah;
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Ira, an Ithrite; Gareb, an Ithrite;
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Uriah, a Hittite; Zabad, the son of Ahlai;
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Adina, the son of Shiza, a Reubenite, the leader of the Reubenites, and thirty who were with him;
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Hanan, the son of Maacah; and Joshaphat, a Mithnite;
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Uzzia, an Ashterathite; Shama and Jeiel, the sons of Hotham, an Aroerite;
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Jediael, the son of Shimri; and Joha, his brother, a Tizite;
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Eliel, a Mahavite; and Jeribai and Joshaviah, the sons of Elnaam; and Ithmah, a Moabite;
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel, and Obed, and Jaasiel from Mezobaite.

< 1 Tarihi 11 >