< 1 Tarihi 11 >

1 Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
Israel pum te Hebron kah David taengla tingtun uh tih, “Kaimih he na rhuh neh na saa ni he.
2 A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
Hlaem hlavai kah na manghai Saul a om vaengah pataeng Israel te na vuenva puei tih na kunael puei. Te dongah ni na Pathen BOEIPA loh namah taengah, ‘Nang tah ka pilnam Israel na luem puei vetih nang he ka pilnam Israel soah rhaengsang la na om ni,’ a ti,” a ti na uh.
3 Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
Israel kah a ham boeih khaw Hebron kah manghai taengla pawk uh tih David loh amih neh Hebron kah BOEIPA mikhmuh ah paipi a saii. Te phoeiah Samuel kut dongkah BOEIPA ol vanbangla David te Israel sokah manghai la a koelh uh.
4 Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
Te vaengah David neh Israel boeih tah Jebus Jerusalem la cet uh. Te khohmuen kah khosa rhoek tah Jebusi rhoek ni.
5 suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
Te vaengah Jebus kah khosa rhoek loh David te, “Hela ha kun boeh,” a ti nah. Tedae David loh David khopuei kah Zion rhalvong te a rhawt pah.
6 Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
Te phoeiah David loh, “Lamhma la Jebusi aka ngawn boeih tah boeilu la, mangpa la om saeh,” a ti nah. Te dongah Zeruiah capa Joab te lamhma la cet tih boeilu la pahoi om van.
7 Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
David loh te kah rhalmahim ah kho a sak dongah ni David khopuei la a khue uh.
8 Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
Khopuei te a kaepvai kah vaikhap lamloh khotaeng khovai hil a thoh tih a caknoi khopuei te Joab loh a hing sak.
9 Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
David te pongpa, pongpa tih a pantai vanbangla caempuei BOEIPA khaw anih taengah om.
10 Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
He tah a ram khuiah anih aka duel David kah boeilu hlangrhalh rhoek neh Israel sokah BOEIPA ol bangla anih aka manghai sak Israel cungkuem rhoek coeng ni.
11 Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
David kah hlangrhalh hlangmi he tah sawmthum kah boeilu, rhalboei Hakhomi capa Jashobeam. Anih loh a caai te a haeng tih ya thum te voei khat la a rhokpam sak.
12 Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
Anih hmatoeng ah Akhohi Dodo capa Eleazar. Anih khaw hlangrhalh pathum khuikah ni.
13 Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
Anih te Pasdammin ah khaw David taengah ni a om. Te vaengah Philisti rhoek tah caemtloek la pahoi tingtun uh. Lohma kah khamyai te cangtun khawk om pueng dae pilnam tah Philisti mikhmuh lamloh rhaelrham uh.
14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
Lohma li ah pai uh tih khohmuen te a huul uh. Te dongah Philisti te a ngawn uh vaengah khaw BOEIPA loh loeihnah a len neh a khang.
15 Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
Boeilu sawmthum lamkah pathum te Adullam lungko lungpang kah David taengla a suntlak uh vaengah Philisti caem tah Rephaim kol ah rhaeh uh.
16 A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
David te rhalvong ah a om kuelhuelh vaengah Philisti khohung te Bethlehem ah om van.
17 Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
David loh Bethlehem vongka kah tuito lamkah tui te a ngaidam, a ngaidam vaengah tah, “Kai he u long nim n'tul lah ve?” a ti.
18 Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
Pathum long te Philisti rhaehhmuen te a va uh tih vongka taengkah Bethlehem tuito lamkah tui te a than uh. Te phoeiah a khuen uh tih David taengla pawk uh. Tedae David loh te te a ok ham huem pawt tih BOEIPA ham a suep.
19 Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
Te phoeiah, “He saii ham he kamah lamkah khaw, ka Pathen taeng lamkah khaw savisava saeh. A hinglu te a kun puei uh coeng dongah hinglu dongkah hlang thii he a ka ok eh?” a ti. Te dongah hlangrhalh pathum loh a saii pah te ok hamla huem pawh.
20 Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
Te vaengah Joab mana Abishai tah te rhoek pathum kah a lu la om. Anih loh a caai a haeng tih ya thum te a rhokpam sak. Te dongah pawt nim anih te pathum lakli ah ming a om.
21 Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
Pathum lakah khaw rhaep nit la a thangpom tih amih taengah mangpa la a om coeng dongah pathum lakli ah mop voel pawh.
22 Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
Kabzeel lamkah bisai aka ping, tatthai hlang capa, Jehoiada koca Benaiah loh Moab kah sathueng hlang rhoi te a tloek. Te phoeiah anih te vuelsong khohnin ah khaw suntla tih tangrhom khui kah sathueng te a ngawn bal.
23 Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
Anih loh Egypt hlang te khaw a ngawn. Tekah hlang te cungnueh ah dong nga lo. Egypt kut dongkah caai te hni tak kah tampai bangla om. Tedae anih te conghol neh a suntlak thil mai tih Egypt kut lamkah caai te a rhawth pah. Te phoeiah amah caai neh amah te a ngawn.
24 Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
He tlam he Jehoiada capa Benaiah loh a saii dongah ni anih te a ming khaw hlangrhalh pathum lakah a om.
25 Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
Sawmthum lakah khaw anih te amah la thangpom coeng ne. Tedae pathum taengla a mop thai voel pawt dongah anih te David loh a taengom la a khueh.
26 Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
Te vaengkah tatthai hlangrhalh rhoek tah Joab mana Asahel, Bethlehem lamkah Dodo capa Elhanan.
27 Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
Haroree Shammoth, Pelonee Helez.
28 Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
Tekoa Ikkesh capa Ira, Anatoth Abiezer.
29 Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
Khushathi Sibbekhai neh Akhohi Ilai.
30 Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
Netophah Maharai neh Netophah Baanah capa Heled.
31 Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
Benjamin koca Gibeah lamkah Ribai capa Ittai. Pirathon kah Benaiah.
32 Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
Gaash soklong lamkah Hurai neh Arbahi Abiel.
33 Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
Baharumi Azmaveth neh Shaalbin Eliaba.
34 ’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
Gizoni Hashem koca rhoek ah Harari Shagee capa Jonathan.
35 Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
Harari Sakar capa Ahiam, Ur capa Eliphal.
36 Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
Mekerathi Hepher neh Pelonee Ahijah.
37 Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
Karmel Hezro neh Ezbai capa Naari.
38 Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
Nathan mana Joel neh Hagri capa Mibhar.
39 Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
Ammoni Zelek neh Zeruiah capa Joab kah hno phuei Beeroth Naharai.
40 Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
Yitha Ira neh Yitha Gareb.
41 Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
Khitti Uriah neh Ahlai capa Zabad.
42 Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
Reuben boeilu Reuben Shiza capa Adina neh a taengkah sawmthum.
43 Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
Maakah capa Hanan neh Mithini Joshaphat.
44 Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
Ashtrarity Uzzia, Shamma, Jeuel neh Jeiel. Arori Hotham koca rhoek.
45 Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
Shimri capa Jediael neh a mana Tizi Joha.
46 Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
Makhavim Eliel, Jeribai, Elnaam koca Joshavi, Moab Ithmah.
47 Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.
Eliel, Obed neh Mezobah Jaasiel.

< 1 Tarihi 11 >