< Psalm 92 >

1 Ein Psalm. Ein Lied, für den Sabbattag. Köstlich ist's, Jahwe zu danken und deinem Namen zu lobsingen, du Höchster,
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 am Morgen deine Gnade zu verkündigen und deine Treue in den Nächten
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 zum zehnsaitigen Psalter und zur Harfe, zu Saitenspiel auf der Zither.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 Denn du hast mich fröhlich gemacht, Jahwe, durch dein Thun; ich juble über die Werke deiner Hände.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 Wie sind deine Werke so groß, Jahwe, deine Gedanken so sehr tief!
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 Der tierische Mensch erkennt es nicht, und der Thor begreift es nicht.
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 Wenn die Gottlosen wie das Gras sprossen, und alle Übelthäter blühen, so geschieht das, damit sie für immer vertilgt werden.
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 Du aber, Jahwe, thronst auf ewig in der Himmelshöhe.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 Denn fürwahr, deine Feinde, Jahwe, denn fürwahr, deine Feinde werden vergehen, alle Übelthäter werden sich zerstreuen.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 Und du ließest mein Horn hoch erhoben sein wie das eines Wildochsen, kräftigtest mein Alter durch frisches Öl.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 Mein Auge blickte mit Lust auf meine Feinde, und meine Ohren hörten ihre Freude an den Bösewichtern, die sich wider mich erhoben hatten.
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 Der Fromme sproßt wie die Palme; er wächst wie die Ceder auf dem Libanon.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 Im Tempel Jahwes gepflanzt, treiben sie in den Vorhöfen unseres Gottes Sprossen.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 Noch im Alter tragen sie Frucht, sind saftvoll und frisch,
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 zu verkünden, daß Jahwe gerecht ist, mein Fels, an dem kein Unrecht ist.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Psalm 92 >