< Psalm 83 >

1 Ein Lied. Ein Psalm Asaphs. O Gott, sei nicht länger still; schweige nicht und bleibe nicht ruhig, o Gott!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Denn fürwahr, deine Feinde toben, und die dich hassen, erheben das Haupt.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 Wider dein Volk machen sie listigen Anschlag und beraten sich wider die von dir Geborgenen.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 Sie sprechen: “Wohlan, wir wollen sie vertilgen, daß sie kein Volk mehr seien, und des Namens Israel fortan nicht mehr gedacht werde!”
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Denn sie haben sich einmütig beraten und schlossen einen Bund wider dich,
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 die Zelte Edoms und der Ismaeliter, Moabs und der Hagriter,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal und Ammon und Amalek, Philistäa samt den Bewohnern von Tyrus.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 Auch Assur hat sich zu ihnen geschlagen; sie leihen den Söhnen Lots ihren Arm. (Sela)
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Thue ihnen, wie Midian, wie Sisera, wie Jabin am Bache Kison.
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 Sie wurden vertilgt bei Endor, wurden Dünger für das Land.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 Mache sie, ihre Edlen, wie Oreb und wie Seeb und alle ihre Fürsten wie Sebah und Zalmunna.
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 Sie, die da sprachen: Wir wollen für uns in Besitz nehmen die Auen Gottes!
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Mein Gott, mache sie gleich wirbelndem Staube, gleich Stoppeln vor dem Winde.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Wie Feuer, das den Wald entzündet, und wie eine Flamme, die Berge verbrennt,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 so verfolge sie mit deinem Wetter und schrecke sie mit deiner Windsbraut!
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Mache ihr Angesicht voll Schmach, damit sie deinen Namen suchen, Jahwe.
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Laß sie beschämt und erschreckt werden für immer; laß sie zu Schanden werden und zu Grunde gehn,
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 damit sie inne werden, daß du Jahwe heißest, du allein erhaben bist über die ganze Erde!
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.

< Psalm 83 >