< Psalm 114 >

1 Als Israel aus Ägypten zog, das Haus Jakobs aus dem unverständlich redenden Volke,
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 da ward Juda sein Heiligtum, Israel sein Herrschaftsbereich.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 Das Meer sah ihn und floh, der Jordan wandte sich zurück.
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 Die Berge hüpften wie Widder, die Hügel wie Lämmer.
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 Was ist dir, o Meer, daß du fliehst, du Jordan, daß du dich zurückwendest?
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 Ihr Berge, daß ihr wie Widder hüpft, ihr Hügel wie Lämmer?
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 Vor dem Angesichte des Herrn erbebe, du Erde, vor dem Angesichte des Gottes Jakobs,
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 der den Felsen in einen Wasserteich verwandelt, den Kieselstein in einen Wasserquell.
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.

< Psalm 114 >