< Nehemia 7 >

1 Als nun die Mauer gebaut war, setzte ich die Thüren ein, und es wurden die Thorhüter mit der Aufsicht betraut.
Bayan an sāke gina katangar na kuma sa ƙofofi a wurarensu, sai aka naɗa masu tsaro, da mawaƙa, da Lawiyawa.
2 Und ich beorderte zu Befehlshabern über Jerusalem meinen Bruder Hanani und Hananja, den Obersten der Burg; denn er war ein so zuverlässiger und gottesfürchtiger Mann, wie wenige.
Na sa ɗan’uwana Hanani tare da Hananiya shugaban fada aikin riƙon Urushalima, domin shi Hananiya mutum mai mutunci ne, mai tsoron Allah fiye da yawancin mutane.
3 Und ich wies sie an: Die Thore Jerusalems dürfen nicht eher geöffnet werden, als bis die Sonne heiß scheint. Und während die Wachtposten noch dastehen, soll man die Thürflügel schließen und verriegeln. Und dann soll man Wachen aus den Einwohnern Jerusalems aufstellen, einen jeden auf seinem Posten und zwar einen jeden gegenüber seinem Hause.
Na ce musu, “Kada a buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe sai rana ta fito sosai. Yayinda matsaran ƙofofi suna aiki, a kulle ƙofofin a sa musu sakata kafin matsaran su tashi, wajen fāɗuwar rana. Ku kuma naɗa mazaunan Urushalima a matsayin masu tsaro, waɗansunsu a wuraren aiki, waɗansun kuma kusa da gidajensu.”
4 Es war aber die Stadt von großer Ausdehnung, jedoch nur wenig Volks in ihr, und manche Häuser waren nicht wieder aufgebaut.
Birnin Urushalima kuwa tana da fāɗi da girma, amma mutanen da suke zama a cikinta kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje da yawa ba tukuna.
5 Da gab mir mein Gott in den Sinn, die Edlen und die Vorsteher und das Volk zur Anfertigung eines Geschlechtsverzeichnisses zu versammeln. Da fand ich das Geschlechtsbuch derer, die zuerst heraufgezogen waren, und fand darin geschrieben:
Sai Allahna ya sa a zuciyata in tara manyan gari, shugabanni da talakawa don a rubuta su bisa ga iyalansu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara dawowa. Ga abin da na tarar an rubuta a ciki.
6 Dies sind die Angehörigen der Provinz Juda, die aus der Gefangenschaft der Weggeführten, die Nebukadnezar, der König von Babel, weggeführt hatte, heraufzogen und nach Jerusalem und Juda, ein jeder in seine Stadt, heimkehrten,
Waɗannan su ne mutanen yankin da suka dawo daga zaman bautar da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kame (sun dawo Urushalima da Yahuda, kowanne zuwa garinsa.
7 die mit Serubabel, Jesua, Nehemia, Asarja, Raamja, Nahemani, Mardochai, Bilsan, Mispereth, Bigevai, Nehum und Baana kamen. Die Zahl der Männer des Volkes Israel betrug:
Sun dawo tare da Zerubbabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Azariya, da Ra’amiya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Nehum da kuma Ba’ana). Ga jerin mutanen Isra’ila.
8 Die Nachkommen Pareos': 2172.
Zuriyar Farosh mutum 2,172
9 Die Nachkommen Sephatjas: 372.
ta Shefatiya 372
10 Die Nachkommen Arahs: 652.
ta Ara 652
11 Die Nachkommen Pahath-Moabs, nämlich die Nachkommen Jesuas und Joabs: 2818.
ta Fahat-Mowab (ta wurin Yeshuwa da Yowab) 2,818
12 Die Nachkommen Elams: 1254.
ta Elam 1,254
13 Die Nachkommen Sattus: 845.
ta Zattu 845
14 Die Nachkommen Sakkais: 760.
ta Zakkai 760
15 Die Nachkommen Binnuis: 648.
ta Binnuyi 648
16 Die Nachkommen Bebais: 628.
ta Bebai 628
17 Die Nachkommen Asgads: 2322.
ta Azgad 2,322
18 Die Nachkommen Adonikams: 667.
ta Adonikam 667
19 Die Nachkommen Bigevais: 2067.
ta Bigwai 2,067
20 Die Nachkommen Adins: 655.
ta Adin 655
21 Die Nachkommen Aters von Hiskia: 98.
ta Ater (ta wurin Hezekiya) 98
22 Die Nachkommen Hasums: 328.
ta Hashum 328
23 Die Nachkommen Bezais: 324.
ta Bezai 324
24 Die Nachkommen Hariphs: 112.
ta Harif 112
25 Die Leute von Gibeon: 95.
ta Gibeyon 95.
26 Die Leute von Bethlehem und Netopha: 188.
Mutanen Betlehem da na Netofa 188
27 Die Leute von Anathoth: 128.
na Anatot 128
28 Die Männer von Beth-Asmaveth: 42.
na Bet-Azmawet 42
29 Die Männer von Kirjath-Jearim, Kaphira und Beeroth: 743.
na Kiriyat Yeyarim, Kefira da na Beyerot 743
30 Die Männer von Rama und Geba: 621.
na Rama da na Geba 621
31 Die Männer von Michmas: 122.
na Mikmash 122
32 Die Männer von Bethel und Ai: 123.
na Betel da na Ai 123
33 Die Männer von Nebo: 52.
na ɗayan Nebo 52
34 Die Nachkommen des anderen Elam: 1254.
na ɗayan Elam 1,254
35 Die Nachkommen Harims: 320.
na Harim 2 320
36 Die Leute von Jericho: 345.
na Yeriko 345
37 Die Leute von Lod, Hadid und Ono: 721.
na Lod, da na Hadid, da na Ono 721
38 Die Leute von Senaa: 3930.
na Sena’a 3,930.
39 Die Priester: Die Nachkommen Jedajas vom Hause Jesua: 973.
Ga zuriyar Firistoci. Zuriyar Yedahiya (ta wurin iyalin Yeshuwa) 973
40 Die Nachkommen Immers: 1052.
ta Immer 1,052
41 Die Nachkommen Pashurs: 1247.
ta Fashhur 1,247
42 Die Nachkommen Harims: 1017.
ta Harim 1,017.
43 Die Leviten: Die Nachkommen Jesuas und Kadmiels, von den Nachkommen Hodejas: 74.
Ga zuriyar Lawiyawa. Zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel (ta wurin Hodeba) 74.
44 Die Sänger: Die Nachkommen Asaphs: 148.
Mawaƙa. Zuriyar Asaf mutum 148.
45 Die Thorhüter: Die Nachkommen Sallums, die Nachkommen Aters, die Nachkommen Talmons, die Nachkommen Akkubs, die Nachkommen Hatitas, die Nachkommen Sobais: 138.
Ga zuriyar Matsaran Ƙofofi. Zuriyar Shallum, Ater, Talmon, Akkub, Hatita da Shobai 138.
46 Die Tempeldiener: Die Nachkommen Zihas, die Nachkommen Hasuphas, die Nachkommen Tabbaoths,
Ma’aikatan haikali. Zuriyar Ziha, Hasufa, Tabbawot,
47 die Nachkommen Keros', die Nachkommen Sias, die Nachkommen Padons,
da ta Keros, da ta Siya, da ta Fadon,
48 die Nachkommen Lebanas, die Nachkommen Hagabas, die Nachkommen Salmais,
da ta Lebana, da ta Hagaba, da ta Shalmai,
49 die Nachkommen Hanans, die Nachkommen Giddels, die Nachkommen Gahars,
da ta Hanan, da ta Giddel, da ta Gahar,
50 die Nachkommen Reajas, die Nachkommen Rezins, die Nachkommen Nekodas,
da ta Reyahiya, da ta Rezin, da ta Nekoda,
51 die Nachkommen Gassams, die Nachkommen Usas, die Nachkommen Paseahs,
da ta Gazzam, da ta Uzza, da ta Faseya,
52 die Nachkommen Besais, die Nachkommen der Meuniter, die Nachkommen der Nephisiter,
da ta Besai, da ta Meyunawa, da ta Nefussiyawa,
53 die Nachkommen Bakbuks, die Nachkommen Kauphas, die Nachkommen Harhurs,
da ta Bakbuk, da ta Hakufa, da ta Harhur,
54 die Nachkommen Bazeliths, die Nachkommen Mehidas, die Nachkommen Harsas,
da ta Bazlit, da ta Mehida, da ta Harsha,
55 die Nachkommen Barkos', die Nachkommen Siseras, die Nachkommen Themahs,
da ta Barkos, da ta Sisera, da ta Tema,
56 die Nachkommen Neziahs, die Nachkommen Hatiphas.
da ta Neziya, da kuma ta Hatifa.
57 Die Nachkommen der Sklaven Salomos: Die Nachkommen Sotais, die Nachkommen Sophereths, die Nachkommen Peridas,
Ga zuriyar bayin Solomon. Zuriyar Sotai, da ta Soferet, da ta Ferida,
58 die Nachkommen Jaalas, die Nachkommen Darkons, die Nachkommen Giddels,
da ta Ya’ala, da ta Darkon, da ta Giddel,
59 die Nachkommen Sephatjas, die Nachkommen Hattils, die Nachkommen des Pochereth-Hazzebaim, die Nachkommen Amons,
Shefatiya, Hattil, Fokeret-Hazzebayim, da Amon.
60 sämtliche Tempeldiener und Nachkommen der Sklaven Salomos: 392.
Zuriyar ma’aikatan haikali da ta bayin Solomon su 392.
61 Und diese sind es, die aus Tel-Melah, Tel-Harsa, Cherub, Addon und Immer heraufzogen, ohne daß sie ihre Familie und ihre Abstammung angeben konnten, ob sie aus Israel stammten:
Waɗansu sun hauro daga garuruwan Tel-Mela, Tel-Harsha, Kerub, Addon da Immer, amma ba su iya nuna cewa iyalansu su zuriyar Isra’ila ce ba,
62 Die Nachkommen Delajas, die Nachkommen Tobias, die Nachkommen Nekodas: 642.
zuriyar Delahiya, Tobiya, da Nekoda 642.
63 Und von den Priestern: Die Nachkommen Habajas, die Nachkommen Hakkoz', die Nachkommen Barsillais, der eine von den Töchtern des Gileaditers Barsillai geheiratet hatte und nach ihrem Namen genannt wurde.
Na wajen firistoci kuwa su ne, Zuriyar Hobahiya, da ta Hakkoz, da ta Barzillai (wani mutumin da ya auri’yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kuma kira shi da wannan suna).
64 Diese suchten ihre Geschlechtsverzeichnisse, aber sie waren nicht zu finden; daher wurden sie vom Priestertum ausgeschlossen.
Waɗannan ne aka nemi sunayensu a cikin tarihin asalin iyalai, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki.
65 Und der Statthalter verbot ihnen, vom Hochheiligen zu essen, bis wieder ein Priester für die Handhabung der Urim und Tummim erstehen würde.
Sai gwamna ya umarce su kada su ci wani abinci mafi tsarki, sai akwai firist da zai nemi nufin Ubangiji ta wurin Urim da Tummim.
66 Die ganze Gemeinde betrug zusammen 42360,
Yawan jama’ar duka ya kai mutum 42,360,
67 ungerechnet ihre Sklaven und Sklavinnen; deren gab es 7337 und dazu kamen 245 Sänger und Sängerinnen.
ban da bayinsu maza da mata 7,337. Suna kuma da mawaƙa maza da mata 245.
68 Rosse hatten sie: 736, Maultiere: 245,
Akwai dawakai 736, alfadarai 245
69 Kamele: 435, Esel: 6720.
raƙuma 435, da kuma jakuna 6,720.
70 Und ein Teil der Familienhäupter spendete zum Tempeldienst. Der Statthalter spendete für den Schatz: an Gold tausend Drachmen, fünfzig Sprengschalen, 30 Priesterröcke.
Waɗansu shugabannin iyalai suka ba da kyautai domin taimakon aiki. Gwamna ya ba da darik 1,000 na zinariya, kwanoni 50, da riguna 530 don firistoci.
71 Und einige von den Familienhäuptern spendeten zum Schatze für den Tempeldienst: an Gold 20000 Drachmen und an Silber 2200 Minen.
Waɗansu shugabannin iyalai sun ba da darik 20,000 na zinariya da mina 2,200 na azurfa don aiki.
72 Und was das übrige Volk spendete, betrug an Gold 20000 Drachmen und an Silber 2000 Minen, und siebenundsechzig Priesterröcke.
Jimillar da sauran mutane suka bayar ta kai darik 20,000 na zinariya, minas 2,000 na azurfa, da riguna sittin da bakwai don firistoci.
73 Und so wohnten die Priester und die Leviten und die Thorhüter und die Sänger und ein Teil des Volks und die Tempeldiener und sämtliche Israeliten in ihren Städten.
Firistoci, da Lawiyawa, da matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da ma’aikatan haikali tare da waɗansu mutane da kuma sauran mutanen Isra’ila, suka zauna a garuruwansu. Da wata na bakwai ya zo, Isra’ilawa kuwa sun riga sun zauna a garuruwansu,

< Nehemia 7 >