< Job 40 >

1 Und Jahwe antwortete Hiob und sprach:
Ubangiji ya ce wa Ayuba,
2 Hadern mit dem Allmächtigen will der Tadler? Der Ankläger Gottes antwortete darauf!
“Mai neman sa wa wani laifi zai iya ja da Maɗaukaki? Bari mai tuhumar Allah yă amsa masa.”
3 Dann antwortete Hiob Jahwe und sprach:
Sai Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
4 Fürwahr, zu gering bin ich; was soll ich dir erwidern? Ich lege meine Hand auf meinen Mund.
“Ai, ni ba a bakin kome nake ba ne, ta yaya zan iya amsa maka? Na rufe bakina da hannuna.
5 Einmal habe ich geredet und werde es nicht wiederholen - ein zweites Mal, und werde es nicht wieder thun!
Na yi magana sau ɗaya amma ba ni da amsa, sau biyu, amma ba zan ƙara cewa kome ba.”
6 Dann antwortete Jahwe Hiob aus Wettersturm und sprach:
Sa’an nan Ubangiji ya yi wa Ayuba magana ta cikin guguwa,
7 Auf, gürte deine Lenden wie ein Mann: Ich will dich fragen und du belehre mich!
“Ka tashi tsaye ka tsaya da ƙarfi kamar namiji; zan yi maka tambaya kuma za ka amsa mini.
8 Willst du gar mein Recht zunichte machen, mich verdammen, damit du Recht behaltest?
“Ko za ka ƙi yarda da shari’ata? Za ka ba ni laifi don ka nuna kai marar laifi ne?
9 Hast du denn einen Arm wie Gott und vermagst du mit gleichem Schall wie er zu donnern?
Ko hannunka irin na Allah ne, kuma ko muryarka za tă iya tsawa kamar ta Allah?
10 Schmücke dich doch mit Majestät und Hoheit! Umkleide dich mit Glanz und Herrlichkeit!
Sai ka yi wa kanka ado da ɗaukaka da girma, ka yafa daraja da muƙami.
11 Laß sich ergießen deines Zornes Fluten und wirf mit einem Blicke jeden Stolzen nieder!
Ka saki fushinka, ka dubi dukan wani mai girman kai ka wulaƙanta shi.
12 Mit einem Blicke demütige jeden Stolzen und strecke die Gottlosen zu Boden.
Ka dubi duk wani mai girman kai ka ƙasƙantar da shi, ka tattake mugaye a inda ka tsaya.
13 Birg sie im Staube allzumal, banne ihr Angesicht an verborgenem Ort,
Ka bizne su duka tare ka rufe fuskokinsu a cikin kabari.
14 so will auch ich dich loben, daß deine Rechte dir Sieg verschafft!
Sa’an nan ni kaina zan shaida maka cewa hannun damanka zai iya cetonka.
15 Sieh nur das Nilpferd, das ich schuf wie dich; Gras frißt es wie ein Rind!
“Dubi dorina, wadda na halicce ku tare kuma ciyawa take ci kamar sa.
16 Sieh nur seine Kraft in seinen Lenden und seine Stärke in den Muskeln seines Leibes.
Ga shi ƙarfinta yana a ƙugunta ikonta yana cikin tsokar cikinta.
17 Es streckt seinen Schwanz wie eine Ceder aus, die Sehnen seiner Schenkel sind dicht verschlungen.
Wutsiyarta tana da ƙarfi kamar itacen al’ul; jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe a wuri ɗaya.
18 Seine Knochen sind Röhren von Erz, seine Gebeine wie ein eiserner Stab.
Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, haƙarƙarinta kamar sandunan ƙarfe.
19 Das ist der Erstling von Gottes Walten; der es schuf, reicht dar sein Schwert.
Tana ta farko cikin ayyukan Allah, Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkarar ta da takobi.
20 Denn Futter tragen ihm die Berge, wo alle Tiere des Feldes spielen.
Tuddai su suke tanada mata abinci a inda duk namun jeji suke wasa.
21 Unter Lotusbüschen lagert es, im Versteck von Rohr und Schilf.
Tana kwanciya a ƙarƙashin inuwar itacen lotus ta ɓuya cikin kyauro da fadama.
22 Lotusbüsche überdachen es, um ihm Schatten zu geben, des Baches Weiden umfangen es.
Inuwa ta rufe ta da ƙaddaji, itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta.
23 Wenn der Strom anschwillt, bangt es nicht, bleibt ruhig, wenn ein Jordan gegen seinen Rachen andringt.
Sa’ad da kogi ya cika yana hauka, ba tă damu ba; ba abin da zai same ta ko da a gaban bakinta Urdun yake wucewa.
24 Vermag es einer von vorn zu packen, mit Sprenkeln ihm die Nase zu durchbohren?
Ko akwai wanda zai iya kama ta ba ta kallo, ko kuma a kama ta da tarko a huda hancinta?

< Job 40 >