< Psalm 64 >

1 Auf den Siegesspender, ein Lied, von David. Erhör, mein Rufen, Gott! Ich klage. Mein Leben wahre vor des Feindes Schrecken!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
2 Verbirg mich vor der Bösen Rotte, vor dem Gelärm der Missetäter,
Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
3 die ihre Zungen gleich dem Dolche schärfen, ein giftig Wort zum Pfeile machen,
Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
4 um aus Verstecken auf die Wehrlosen zu schießen, sie unvermutet zu erschießen, ohne Scheu!
Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
5 Sie machen für sich Schlimmes aus; sie rühmen sich des Schlingenlegens. "Wer wird sie sehen?" sagen sie.
Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
6 Sie sinnen auf Verbrechen. "Wir denken sie nach allen Seiten aus", so denken sie bei sich im tiefsten Herzensgrunde.
Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
7 Mit Pfeilen treff' sie Gott! Ganz unvermutet sollen ihnen Wunden werden!
Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
8 Sie sollen ihnen ihre Zunge lähmen! Ein jeder schaudere, der dies an ihnen sieht!
Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
9 Dann fürchten sich die andern Menschen alleund künden es als Gottes Tatund rechnen als sein Werk es an.
Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
10 Der Fromme freue sich alsdann des Herrnund baue fest auf ihn, und alle frommen Herzen triumphieren!
Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!

< Psalm 64 >