< Psalm 28 >

1 Von David. - Ich rufe, Herr, zu Dir. Sei doch nicht taub vor mir, mein Hort! Wenn Du vor mir verstummst, dann gleiche ich ins Grab Gesunkenen.
Ta Dawuda. A gare ka nake kira, ya Ubangiji Dutsena; kada ka yi mini kunnen ƙashi. Gama in ka yi shiru, zan zama kamar waɗanda suka gangara rami.
2 Mein lautes Flehen hör, wenn ich, zu Dir um Hilfe rufend, zu Deinem Allerheiligsten die Hände breite!
Ka ji kukata ta neman jinƙai yayinda nake kira ka don neman taimako, yayinda nake daga hannuwana wajen Wurinka Mafi Tsarki.
3 Nicht lange laß mich sein bei Frevlern und nicht bei Übeltätern! Sie reden freundlich mit dem Nächsten; doch sinnen sie im Herzen Böses.
Kada ka ja ni tare da mugaye, tare da masu yin mugunta, masu magana kamar ta alheri ce da maƙwabtansu amma suna riƙe da su a zukatansu.
4 Vergilt Du ihnen ihrer Tat gemäß, nach ihrer bösen Art! Nach ihrer Hände Werk belohne sie! Behandle sie, wie sie's verdienen!
Ka sāka musu da ayyukansu da kuma don mugun aikinsu; ka sāka musu saboda abin da hannuwansu suka yi ka kuma mayar musu abin da ya dace da su.
5 Sie achten nimmer auf des Herren Taten und nicht auf seiner Hände Werk; sie reißen sie herab und bauen sie nicht auf, -
Da yake ba su kula da ayyukan Ubangiji da abin da hannuwansa suka yi ba, zai rushe su ba kuwa zai ƙara gina su ba.
6 Gepriesen sei der Herr, wenn er mein lautes Flehen hört!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji, gama ya ji kukata na neman jinƙai.
7 Der Herr ist mir ein Schutz und Schild; auf ihn vertraut mein Herz. Mir wird geholfen; mein Herz frohlockt. Ich danke ihm mit meinem Liede.
Ubangiji shi ne ƙarfina da garkuwata; zuciyata ta amince da shi, kuma na sami taimako. Zuciyata ta yi tsalle don farin ciki zan kuwa yi godiya gare shi cikin waƙa.
8 Der Herr ist seines Volkes Schutzgott, ein Zufluchtsort, wo sein Gesalbter Hilfe findet.
Ubangiji shi ne ƙarfin mutanensa, kagarar ceto domin shafaffensa.
9 Zuhilfe Deinem Volk! Den ewig Deinen spende Segen! Und weide sie und sorge ewiglich für sie!
Ka cece mutanenka ka kuma albarkace gādonka; ka zama mai kiwonsu ka kuma riƙe su har abada.

< Psalm 28 >