< Sprueche 1 >

1 Die Sprüche Salomos, des Davidssohnes und Herrschers über Israel,
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 sind dazu da, daß man Charakter und Weisheit würdige und kluge Worte wohl verstehe
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 und Zucht und Anstand lerne, was recht und rechtlich, ehrlich sei,
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 daß Bildung Unerfahrene empfangen und daß die Jugend Lebenskunst erlerne.
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 Vernimmt ein Weiser sie, so kann er seine Rede fesselnder gestalten; ein kluger Mann kann sich die richtige Belehrung sichern.
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 Er kann das Gleichnis und den Sinnspruch faßlicher gestalten, wie auch der Weisen Worte, ihre dunklen Reden. -
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 Die Furcht des Herrn ist Anfang der Erkenntnis, Weisheit, Bildung. Nur Toren sind's, die sie verachten.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Der väterlichen Zucht, mein Sohn, gehorche! Der Mutter Mahnung achte nicht gering!
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 Sie zieren wie ein Kranz dein Haupt und deinen Hals wie Kettenschmuck.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Mein Sohn, wenn dich Verbrecher locken, folg ihnen nicht!
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 Wenn sie dir sagen: "Halt's mit uns! Wir haben einen Anschlag gegen einen Menschen vor; wir wollen ungefährdet im Versteck Arglosen auflauern.
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 Wir wollen selbst am Leben bleiben und sie verschlingen gleich der Unterwelt, mit Haut und Haar als solche, die zur Grube fahren. (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 Und wir gewinnen alles mögliche kostbare Gut und füllen unsere Häuser mit dem Raub.
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 Du darfst auch mit uns teilen; wir alle haben einen Beutel."
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 Mein Sohn, geh nicht auf einem Weg mit ihnen! Halt deinen Fuß von ihren Pfaden fern!
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 Denn ihre Füße laufen dem Verderben zu und eilen blutigem Tod entgegen.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Vergeblich wird man Netze spannen vor den Blicken der beschwingten Vögel;
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 sie aber lauern auf ihr eigen Blut und stellen sich selbst nach dem Leben.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 So ist das Schicksal eines jeden, der auf unrechten Gewinn ausgeht. Er bringt ihn um sein Leben.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 Auf Straßen ruft die Weisheit; auf Plätzen ruft sie laut.
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 Hoch oben auf den Mauern predigt sie, an Stadttoren; vor aller Welt nimmt sie das Wort:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 "Wie lange liebt ihr Toren noch Betörung, gefällt den Dünkelhaften Spott und hassen Toren Einsicht?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Ihr kommt auf meine Mahnrede zurück. Fürwahr, ich sag euch unumwunden, was ich auf dem Herzen habe. Ich tue meine Warnungen euch kund.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Ich rief; ihr aber wolltet nicht; ich winkte euch, und niemand gab drauf acht.
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 Ihr schluget meinen Ratschlag in den Wind und mochtet meine Rüge nicht.
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 So lache ich bei eurem Unglück nur und spotte, wenn euch Angst befällt,
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 wenn wie ein Ungewitter euer Schrecken kommt, einherfährt gleich dem Sturmwind euer Unglück und Not und Drangsal euch befällt.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Dann rufen sie mich an; ich gebe keine Antwort. Sie suchen, aber finden mich nicht mehr.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Erkenntnis haben sie gehaßt und nach der Furcht des Herren nicht gefragt,
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 sie wollten nichts von meinem Rate wissen, und meine Rüge haben sie verschmäht.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 So mögen sie denn ihres Handels Frucht genießen, sich sättigen mit dem, was sie sich selbst bereitet!
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 Ihr Fehlgehn bringt sie, diese Dummen, um; Sorglosigkeit vernichtet diese Toren.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 Wer aber mir gehorcht, der kann in Ruhe wohnen und unbesorgt vor Unheilsschrecken sein."
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Sprueche 1 >