< Luc 1 >

1 Comme beaucoup ont entrepris de mettre par ordre le récit des choses qui se sont accomplies parmi nous,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Suivant que nous les ont transmises ceux qui, dès le commencement, les ont eux-mêmes vues, et qui ont été les ministres de la parole;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 J’ai cru, moi aussi, excellent Théophile, après m’être diligemment informé de tout dès l’origine, devoir t’en écrire par ordre toute l’histoire;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Afin que tu connaisses la vérité de ce dont tu as été instruit.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Aux jours d’Hérode, roi de Judée, il y eut un prêtre nommé Zacharie, de la classe d’Abia; et sa femme, d’entre les filles d’Aaron, s’appelait Elisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ils étaient tous deux justes devant Dieu, marchant sans reproche dans les commandements et toutes les lois du Seigneur;
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Et ils n’avaient point de fils, parce que Élisabeth était stérile, et que tous deux étaient avancés en âge.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Or il arriva que lorsque Zacharie remplissait devant Dieu, les fonctions du sacerdoce, au rang de sa classe,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Il lui échut par le sort, suivant la coutume observée entre les prêtres, d’entrer dans le temple du Seigneur pour y offrir l’encens.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Et toute la multitude du peuple était dehors priant, à l’heure de l’encens.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Et un ange du Seigneur lui apparut debout, à droite de l’autel de l’encens.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zacharie fut troublé en le voyant, et la crainte le saisit.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Mais l’ange lui dit: Ne crains point, Zacharie, parce que ta prière a été exaucée; ÉLisabeth, ta femme, enfantera un fils, et tu lui donneras le nom de Jean;
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Il sera pour toi un sujet de joie et d’allégresse, et, à sa naissance, beaucoup se réjouiront.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Car il sera grand devant le Seigneur; il ne boira ni vin ni cervoise, et il sera rempli du Saint-Esprit dès le sein de sa mère;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Et il convertira un grand nombre d’enfants d’Israël au Seigneur leur Dieu;
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Et il marchera devant lui dans l’esprit et la vertu d’Élie, afin qu’il unisse les cœurs des pères à ceux des fils, ramène les incrédules à la prudence des justes, pour préparer ainsi au Seigneur un peuple parfait.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Et Zacharie dit à l’ange: Comment connaîtrai-je cela? car je suis vieux, et ma femme est avancée en âge.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Et l’ange répondant, lui dit: Je suis Gabriel, qui me tiens devant Dieu, et j’ai été envoyé pour te parler et t’annoncer cette heureuse nouvelle.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Et voilà que tu seras muet, et ne pourras parler jusqu’au jour où ces choses arriveront, parce que tu n’as pas cru à mes paroles, qui s’accompliront en leur temps.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Cependant le peuple était dans l’attente de Zacharie, et il s’étonnait qu’il demeurât si longtemps dans le temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Mais étant sorti, il ne pouvait leur parler; et ils comprirent qu’il avait eu une vision dans le temple. Et pour lui, il leur faisait des signes, et il resta muet.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Et il arriva que lorsque les jours de son ministère furent accomplis, il s’en alla en sa maison.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Or après ces jours, Elisabeth, sa femme, conçut, et elle se tenait cachée pendant cinq mois, disant:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 C’est ainsi que le Seigneur a fait pour moi aux jours où il m’a regardée pour me délivrer de mon opprobre parmi les hommes.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Au sixième mois, l’ange Gabriel fut envoyé de Dieu dans la ville de Galilée, appelée Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 À une vierge qu’avait épousée un homme nommé Joseph, de la maison de David; et le nom de la vierge était Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Or l’ange étant venu vers elle lui dit: Je vous salue, pleine de grâce; le Seigneur est avec vous; vous êtes bénie entre les femmes.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Lorsque Marie l’eut entendu, elle fut troublée de ses paroles, et elle pensait quelle pouvait être cette salutation.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Mais l’ange lui dit: Ne craignez point, Marie; vous avez trouvé grâce devant Dieu;
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Voilà que vous concevrez dans votre sein, et vous enfanterez un fils à qui vous donnerez le nom de Jésus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Il sera grand, et sera appelé le Fils du Très-Haut, et le Seigneur Dieu lui donnera le trône de David, son père;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 et il régnera éternellement sur la maison de Jacob, Et son règne n’aura point de fin. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Marie dit à l’ange: Comment cela se fera-t-il? car je ne connais point d’homme.
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Et l’ange répondant, lui dit: L’Esprit-Saint surviendra en vous, et la vertu du Très-Haut vous couvrira de son ombre. C’est pourquoi la chose sainte qui naîtra de vous sera appelée le Fils de Dieu.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Et voilà qu’Élisabeth, votre parente, a conçu, elle aussi, un fils dans sa vieillesse; et ce mois est le sixième de celle qu’on appelle stérile,
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Car, à Dieu, rien n’est impossible.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Alors Marie reprit: Voici la servante du Seigneur, qu’il me soit fait selon votre parole. Et l’ange s’éloigna d’elle.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Or en ces jours-là, Marie, se levant, s’en alla en grande hâte vers les montagnes, en une ville de Juda;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Et elle entra dans la maison de Zacharie, et elle salua Élisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Et il arriva que lorsque Élisabeth entendit la salutation de Marie, l’enfant tressaillit dans son sein, et Élisabeth fut remplie de l’Esprit-Saint;
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Alors elle s’écria d’une voix forte: Vous êtes bénie entre les femmes, et le fruit de votre sein est béni.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Et d’où m’arrive-t-il que la mère de mon Seigneur vienne vers moi?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Car, dès que la voix de votre salutation est venue à mes oreilles, l’enfant a tressailli de joie dans mon sein.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Et bienheureuse, vous qui avez cru! car ce qui vous a été dit par le Seigneur s’accomplira.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Alors Marie dit: Mon âme glorifie le Seigneur.
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Et mon esprit a tressailli d’allégresse en Dieu mon Sauveur;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Parce qu’il a regardé l’humilité de sa servante; et voici que désormais toutes les générations me diront bienheureuse;
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Car celui qui est puissant m’a fait de grandes choses, et son nom est saint;
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Et sa miséricorde se répand d’âge en âge sur ceux qui le craignent.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Il a déployé la force de son bras; il a dissipé ceux qui s’enorgueillissaient dans les pensées de leur cœur.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Il a renversé les puissants de leur trône, et il a élevé les humbles.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Il a rempli de biens les affamés, et il a renvoyé les riches les mains vides.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Se souvenant de sa miséricorde, il a pris sous sa sauvegarde Israël, son serviteur,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 Comme il l’avait promis à nos pères, à Abraham, et à sa postérité pour toujours. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Marie demeura avec Elisabeth environ trois mois, et elle s’en retourna ensuite en sa maison.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Cependant le temps d’enfanter pour Elisabeth s’accomplit, et elle mit au monde un fils.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Et ses voisins et ses parents, ayant appris que Dieu avait signalé en elle sa miséricorde, s’en réjouissaient avec elle.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Or il arriva qu’au huitième jour, ils vinrent pour circoncire l’enfant, et ils le nommaient Zacharie, du nom de son père.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Mais sa mère prenant la parole, dit: Non, mais il s’appellera Jean.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Ils lui dirent: Il n’y a personne dans votre famille qui soit appelé de ce nom.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Et ils demandaient par signes au père comment il voulait qu’on le nommât.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Or, demandant des tablettes, il écrivit: Jean est son nom. Et tous furent dans l’étonnement.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Aussitôt sa bouche s’ouvrit, sa langue se délia, et il parlait, bénissant Dieu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Et la crainte se répandit sur tous leurs voisins, et toutes ces merveilles furent divulguées dans toutes les montagnes de la Judée;
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Et tous ceux qui les entendirent les recueillirent dans leur cœur, disant: Que pensez-vous que sera cet enfant? Car la main du Seigneur était avec lui.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Et Zacharie, son père, fut rempli de l’Esprit-Saint, et prophétisa, disant:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Béni le Seigneur, le Dieu d’Israël! de ce qu’il a visité et racheté son peuple,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Et nous a suscité une corne de salut dans la maison de son serviteur David,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 Comme il a promis par la bouche de ses saints prophètes, qui ont été dès les temps les plus anciens, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 De nous sauver de nos ennemis et de la main de tous ceux qui nous haïssent,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Pour accomplir ses miséricordes envers nos pères, en souvenir de son alliance sainte;
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Selon le serment qu’il a juré à Abraham, notre père, de faire pour nous,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Qu’étant délivrés de nos ennemis, nous le servions sans crainte,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 Dans la sainteté et la justice, marchant devant lui tous les jours de notre vie.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Et toi, petit enfant, tu seras appelé prophète du Très-Haut; car tu marcheras devant la face du Seigneur pour lui préparer les voies;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Pour donner au peuple la science du salut, et pour la rémission de ses péchés,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Par les entrailles de la miséricorde de notre Dieu, avec lesquelles est venu nous visiter le soleil se levant d’en haut,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Pour éclairer ceux qui sont assis dans les ténèbres et l’ombre de la mort, pour diriger nos pieds dans une voie de paix.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Or l’enfant croissait et se fortifiait en esprit; et il demeurait dans les déserts, jusqu’au jour de sa manifestation devant Israël.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luc 1 >