< 2 Rois 13 >

1 En la vingt-troisième année de Joas, fils d’Ochozias, roi de Juda, Joachaz, fils de Jéhu, régna sur Israël dans Samarie, pendant dix-sept ans.
A shekara ta ashirin da uku ta Yowash ɗan Ahaziya, sarkin Yahuda, Yehoyahaz ɗan Yehu, ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuwa yi mulki shekaru goma sha bakwai.
2 Il fit le mal devant le Seigneur, et il suivit les péchés de Jéroboam, fils de Nabath, qui fit pécher Israël, et il ne s’en détourna point.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji ta wurin bin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai kuwa guje musu ba.
3 Et la fureur du Seigneur fut irritée contre Israël, et il les livra à la main d’Hazaël, roi de Syrie, et à la main de Bénadad, fils d’Hazaël, durant tous ses jours.
Saboda haka fushin Ubangiji ya ƙuna a kan Isra’ila, kuma da daɗewa ya sa su a ƙarƙashin ikon Hazayel sarkin Aram da Ben-Hadad ɗansa.
4 Or Joachaz implora la face du Seigneur, et le Seigneur l’écouta; car il vit l’angoisse d’Israël, parce que le roi de Syrie les avait brisés.
Sai Yehoyahaz ya nemi tagomashin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya saurare shi, domin ya gan irin matsin da sarkin Aram yake yi wa Isra’ila.
5 Et le Seigneur donna un sauveur à Israël, et il fut délivré de la main du roi de Syrie; et les enfants d’Israël habitèrent dans leurs tabernacles comme hier et avant-hier.
Sai Ubangiji ya tā da mai ceto wa Isra’ila, suka kuma kuɓuta daga ikon Aram. Ta haka Isra’ilawa suka yi zama a gidajensu yadda suka yi a dā.
6 Cependant ils ne s’écartèrent pas des péchés de la maison de Jéroboam, qui fit pécher Israël; mais ils y marchèrent, puisque même le bois sacré demeura toujours en Samarie.
Sai dai ba su bar yin zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata; suka ci gaba da yinsu. Haka ma, ginshiƙin Ashera ta kasance a tsaye a cikin Samariya.
7 Et il ne resta de peuple à Joachaz que cinquante cavaliers, dix chariots et dix mille hommes de pied; car le roi de Syrie les avait tués et réduits comme la poussière dans un battage d’aire.
Ba abin da ya rage na rundunar Yehoyahaz sai mahayan dawakai hamsin, kekunan yaƙi goma da kuma sojoji ƙasa dubu goma. Gama sarkin Aram ya hallaka sauran, ya kuma yi kaca-kaca da su kamar ƙura a masussuka.
8 Mais le reste des actions de Joachaz, tout ce qu’il a fait, et son courage, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois d’Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehoyahaz, dukan abubuwan da ya yi da kuma nasarorinsa, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
9 Et Joachaz dormit avec ses pères, et on l’ensevelit à Samarie; et Joas, son fils, régna en sa place.
Yehoyahaz ya huta da kakanninsa, aka binne shi a Samariya, Yehowash ɗansa kuma ya gāje shi.
10 En la trente-septième année de Joas, roi de Juda, Joas, fils de Joachaz, régna sur Israël dans Samarie, pendant seize ans;
A shekaru talatin da bakwai ta Yowash sarkin Yahuda, Yehowash ɗan Yehoyahaz ya zama sarkin Isra’ila a Samariya, ya kuma yi mulki shekaru goma sha shida.
11 Et il fit le mal devant le Seigneur: il ne se détourna pas de tous les péchés de Jéroboam, fils de Nabath, qui fit pécher Israël; mais il y marcha.
Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, bai juya ga barin zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, ya ci gaba da yinsu.
12 Mais le reste des actions de Joas, tout ce qu’il a fait, et son courage, et comment il combattit contre Amasias, roi de Juda, n’est-ce pas écrit dans le Livre des actions des jours des rois d’Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Yowash, da dukan abubuwan da ya yi, da kuma nasarorinsa, haɗe da yaƙin da ya yi da Amaziya sarkin Yahuda, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
13 Et Joas dormit avec ses pères; mais Jéroboam s’assit sur son trône. Or Joas fut enseveli à Samarie avec les rois d’Israël.
Yowash ya huta da kakanninsa, Yerobowam kuwa ya gāje shi. Aka binne Yehowash a Samariya tare da sarakunan Isra’ila.
14 Cependant Élisée était malade de la maladie même dont il mourut; et Joas, roi d’Israël, descendit vers lui, et il pleurait devant lui, et disait: Mon père, mon père, vous le char d’Israël et son conducteur.
To, Elisha ya kamu da ciwon da ya kashe shi. Yowash sarkin Isra’ila ya gangara don yă gan shi, ya kuma yi kuka dominsa. Ya yi kuka yana cewa, “Babana! Babana, keken yaƙin Isra’ila da mahayan dawakanta!”
15 Et Élisée lui dit: Apportez-moi un arc et des flèches. Et lorsqu’il lui eut apporté un arc et des flèches,
Elisha ya ce wa Yehowash, “Ka samo baka da kibiyoyi,” ya kuwa yi haka.
16 Élisée dit: Mettez votre main sur cet arc. Et lorsque le roi eut mis sa main, Élisée mit ses mains sur les mains du roi,
Sai ya ce wa Yehowash sarkin Isra’ila, “Ka ɗauki baka a hannunka.” Da ya ɗauka, sai Elisha ya sa hannunsa a hannuwan sarki.
17 Et dit: Ouvrez la fenêtre qui regarde l’orient. Et lorsqu’il l’eut ouverte, Élisée dit: Jetez une flèche. Et il la jeta. Et Élisée reprit: Flèche de salut du Seigneur, flèche de salut contre la Syrie; et vous frapperez la Syrie à Aphec, jusqu’à ce que vous l’exterminiez.
Ya ce masa, “Ka buɗe taga wajen gabas,” sai ya buɗe. Sai Elisha ya ce, “Ka harba!” Sai ya harba. Elisha ya ce, “Kibiyar nasara ta Ubangiji, kibiyar nasara a kan Aram! Za ka hallaka Arameyawa sarai a Afek.”
18 Il dit encore: Prenez les flèches. Lorsque le roi les eut prises, il lui dit de nouveau: Frappez la terre avec un dard. Et lorsqu’il eut frappé trois fois, et qu’il se fut arrêté,
Sa’an nan ya ce, “Ka ɗauki kibiyoyi,” sai sarkin ya ɗauko. Sai Elisha ya ce, “Ka caki ƙasa.” Sai ya caka sau uku sa’an nan ya daina.
19 L’homme de Dieu s’irrita contre lui et dit: Si vous eussiez frappé la terre cinq fois, ou six fois, ou sept fois, vous auriez frappé la Syrie jusqu’à l’extermination; mais maintenant vous la frapperez par trois fois.
Sai mutumin Allah ya yi fushi da shi ya ce, “Da a ce ka caki ƙasar sau biyar ko shida; da za ka yi nasara a kan Aram ka kuma hallaka ta sarai. Amma yanzu za ka yi nasara a kanta sau uku ne kawai.”
20 Élisée mourut donc, et on l’ensevelit. Or des voleurs de Moab vinrent sur la terre d’Israël en cette même année.
Elisha ya mutu, aka kuma binne shi. To, mahara Mowabawa sun saba kawo hari a ƙasar Isra’ila a kowace bazara.
21 Or quelques hommes enterrant un mort virent les voleurs, et jetèrent le cadavre dans le sépulcre d’Élisée. Lorsque le cadavre eut touché les os d’Élisée, l’homme revécut, et se tint sur ses pieds.
Wata rana yayinda waɗansu Isra’ilawa suke binne wani mutum, farat ɗaya sai ga mahara; saboda haka suka jefar da gawar mutumin a kabarin Elisha. Da gawar ta taɓa ƙasusuwan Elisha, sai mutumin ya farka, ya tashi ya tsaya da ƙafafunsa.
22 Hazaël, roi de Syrie, affligea donc Israël durant tous les jours de Joachaz;
Hazayel sarkin Aram ya musguna wa Isra’ila a duk tsawon mulkin Yehoyahaz.
23 Et le. Seigneur eut pitié d’eux, et il revint à eux à cause de son alliance qu’il avait faite avec Abraham, Isaac et Jacob: il ne voulut pas les perdre, ni les rejeter entièrement jusqu’au temps présent.
Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, ya kuma damu da su saboda alkawarinsa da Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Har yă zuwa yau bai yarda yă hallaka su ko yă shafe su daga gabansa ba.
24 Cependant Hazaël, roi de Syrie, mourut, et Bénadad, son fils, régna en sa place.
Hazayel sarkin Aram ya mutu, sai Ben-Hadad ɗansa ya gāje shi.
25 Mais Joas, fils de Joachaz, reprit de la main de Bénadad, fils d’Hazaël, les villes qu’Hazaël avait prises de la main de Joachaz, son père, par le droit de la guerre. Joas le battit par trois fois, et il rendit les villes d’Israël.
Sa’an nan Yowash ya sāke ƙwato garuruwan da Ben-Hadad ya ci da yaƙi a hannun mahaifinsa Yehoyahaz. Sau uku Yehowash ya yi nasara a kansa, ta haka kuwa ya ƙwace garuruwan Isra’ilawa.

< 2 Rois 13 >