< Marc 3 >

1 Une autre fois, Jésus entra dans une synagogue, où se trouvait un homme qui avait la main desséchée.
Sai kuma ya sake tafiya cikin Majami'a sai ga wani Mutum mai shanyayyen hannu.
2 Les pharisiens l'observaient pour voir s'il le guérirait un jour de sabbat, afin de pouvoir l'accuser.
Wadansu mutane suna kallonsa sosai, su gani ko zai warkar da shi a ranar Asabar. don su zarge shi.
3 Il dit à l'homme qui avait la main desséchée: Lève-toi et tiens-toi au milieu de nous.
Yesu ya ce wa mai shanyayyen hanun “Ka tashi ka tsaya a tsakiyar kowa.”
4 Puis il leur dit: Est-il permis, le jour du sabbat, de faire du bien ou de faire du mal; de sauver une personne ou de la tuer? Mais ils gardaient le silence.
Sai ya ce wa mutane, “Ya dace a yi abu mai kyau aranar Asabar ko a yi mugunta; a ceci rai, ko a yi kisa? “Amma suka yi shiru.
5 Alors, promenant sur eux ses regards avec indignation, et affligé de l'endurcissement de leur coeur, il dit à l'homme: Étends ta main. Il l'étendit, et sa main redevint saine.
Sai ya dube su cikin fushi, yana bakin ciki da taurin zuciyar su, ya ce wa mutumin ka mikar da hanunka, sai ya mikar da hanunsa Yesu kuwa ya warkar da shi.
6 Les pharisiens, étant sortis, tinrent aussitôt conseil avec les hérodiens contre lui, pour le faire périr.
Sai Farisiyawa suka fita da sauri zuwa wurin mutanen Hirudus suka shirya yadda za su kashe shi.
7 Jésus se retira avec ses disciples du côté de la mer, et une grande multitude, venue de la Galilée, le suivit. De la Judée aussi,
Sai Yesu da almajiransa, suka tafi bakin teku. sai mutane dayawa suka bi shi, daga Galili da Yahudiya
8 de Jérusalem, de l'Idumée, du pays au-delà du Jourdain, ainsi que des environs de Tyr et de Sidon, une grande multitude, ayant entendu parler de tout ce qu'il faisait, vint vers lui.
Daga Urushalima da Edom gaba da Urdun da kewayan Taya da Sidon, da baban taro, ya ji abinda yake yi. suka zo wurinsa.
9 Alors il dit à ses disciples de lui tenir une petite barque toute prête, à cause de la foule, pour ne pas être trop pressé par elle.
Ya tambayi almajiransa su shirya masa karamin jirgin ruwa domin yawan mutane, domin kada su murkushe shi.
10 Car il avait guéri plusieurs malades, de sorte que tous ceux qui avaient quelque mal se jetaient sur lui pour le toucher.
Ya warkar da mutane da yawa, yadda duk wadanda suke da cuttutuka suna kokari su taba shi.
11 Et quand les esprits impurs le voyaient, ils tombaient à ses pieds et s'écriaient: Tu es le Fils de Dieu!
Duk sa'adda kazaman ruhohin suka ganshi, sai su durkusa a gabansa su yi ihu da karfi su ce, kai Dan Allah ne.”
12 Mais il leur défendait sévèrement de le faire connaître.
Ya umarce su da karfi kada su sa a san shi.
13 Il alla ensuite sur la montagne, et il appela ceux qu'il voulut choisir lui-même, et ils vinrent à lui.
Ya hau saman dutsen, ya kira wadanda yake bukar su, su zo wurinsa.
14 Il en désigna douze, qu'il nomma apôtres, pour les avoir avec lui et pour les envoyer prêcher,
Ya zabi guda goma sha biyu (ya kira su manzanni). Wadanda zasu kasance tare da shi, ya kuma aike su, su yi wa, azi,
15 avec le pouvoir de chasser les démons.
Ya kuma basu Ikon fitar da aljanu.
16 Voici les douze qu'il désigna: Simon, à qui il donna le nom de Pierre;
Ya zabi guda goma sha biyu wato Saminu kuma yaba shi suna Bitrus.
17 Jacques, fils de Zébédée, et Jean, frère de Jacques, auxquels il donna le nom de Boanerges, c'est-à-dire fils du tonnerre;
Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan-uwan Yakubu wanda ya basu sunan Buwanarjis watau 'ya'yan tsawa,
18 André, Philippe, Barthélémy, Matthieu, Thomas, Jacques, fils d'Alphée, Thaddée, Simon le Cananéen,
da Andarawus da Filibus da Bartalamawus da Matta da Toma da Yakubu dan Halfa, da Taddawus da Saminu Ba-kananiye,
19 et Judas Iscariote, celui-là même qui le trahit.
da Yahuza Iskariyoti wanda zai bashe shi.
20 Jésus entra dans une maison avec ses disciples; et la foule s'y rassembla encore, de sorte qu'ils ne pouvaient pas même prendre leur repas.
Sa'adda ya shiga gida, Taron kuwa ya sake haduwa, har ya hana su cin abinci,
21 Quand ses proches l'eurent appris, ils vinrent pour s'emparer de lui; car ils disaient qu'il avait perdu l'esprit.
Da iyalansa suka ji haka, sai suka fito sun kamo shi, saboda sun ce, “Ai, baya cikin hankalinsa “
22 Les scribes, descendus de Jérusalem, disaient: Il est possédé de Béelzébul, et il chasse les démons par le prince des démons!
Marubutan da suka zo daga Urushalima suka ce “Ai Ba'alzabuba ne ya hau shi, da ikon sarkin aljannu kuma yake fitar da aljannu.”
23 Mais Jésus, les ayant appelés, leur dit en paraboles: Comment Satan pourrait-il chasser Satan?
Yesu ya kirawo su wurinsa ya ce da su cikin misalai, “Yaya shaidan zai iya fitar da shaidan?
24 Si un royaume est divisé contre lui-même, ce royaume-là ne peut subsister;
idan mulki ya rabu gida biyu ba zai tsayawa ba.
25 et si une maison est divisée contre elle-même, cette maison-là ne saurait subsister.
Haka in gida ya rabu kashi biyu, gaba da kansa bai zai tsaya ba.
26 Si donc Satan s'élève contre lui-même, il est divisé et il ne peut subsister, mais il est près de sa fin.
Shaidan kuma in ya tayar wa kansa ya rabu, ba zai iya tsayawa ba, gama karshen sa ya zo kenan.
27 Nul ne peut entrer dans la maison de l'homme fort et piller son bien, s'il n'a auparavant lié cet homme fort; après cela, il pourra piller sa maison.
Amma ba mai iya shiga gidan kakkarfan mutum ya kwace kayansa, ba tare da ya fara daure kakkarfan mutumin ba, sa'an nan kuma ya kwashe kayan gidansa.
28 En vérité, je vous le dis, tous les péchés seront pardonnés aux enfants des hommes, ainsi que tous les blasphèmes qu'ils auront proférés;
Hakika, ina gaya maku, dukan zunuban da mutane suka yi za a gafarta masu, da kowane irin sabon da suka furta,
29 mais tout homme qui aura blasphémé contre le Saint-Esprit, n'en obtiendra jamais le pardon; il est coupable d'un péché éternel. (aiōn g165, aiōnios g166)
amma fa duk wanda yayi sabon Ruhun Mai Tsarki baza a gafarta masa ba ko kadan, ya zama mai zunubi har abada.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Jésus parla ainsi, parce qu'ils disaient: Il est possédé d'un esprit impur.
“Yesu ya fadi wadannan abubuwa domin suna cewa yana da ba kazamin ruhu,”
31 La mère et les frères de Jésus arrivèrent; et, se tenant dehors, ils l'envoyèrent appeler.
Sa'an nan uwatasa, da “Yan'uwansa suka zo suna tsaye a waje. sai suka aika masa, suna kuma umurtar sa ya zo.
32 La foule était assise autour de lui. Et on lui dit: Voici que ta mère et tes frères sont là dehors, qui te cherchent.
Taro kuwa na zaune kewaye da shi, sai suka yi magana da shi da cewa, ga uwarka da yan-uwanka suna nan a waje, suna nemanka.”
33 Mais il répondit: Qui est ma mère, et qui sont mes frères?
Ya amsa masu, “Dacewa su wanene uwa-ta da “yan'uwa na? “
34 Puis, jetant les yeux sur ceux qui étaient assis autour de lui, il dit: Voilà ma mère et mes frères!
Sai ya waiwayi wadanda suke zaune kewaye da shi, yace, “Ga uwa-ta da yan-uwana anan!
35 Quiconque fait la volonté de Dieu, celui-là est mon frère, et ma soeur, et ma mère.
Gama duk wanda ke yin abin da Allah yake so, shine dan'uwana da yar, uwata, da kuma uwa-ta.”

< Marc 3 >