< Marc 3 >

1 Une autre fois, Jésus entra dans une synagogue, où se trouvait un homme qui avait la main desséchée.
Wani lokaci, da ya sāke shiga majami’a, sai ga wani mutum mai shanyayyen hannu.
2 Les pharisiens l'observaient pour voir s'il le guérirait un jour de sabbat, afin de pouvoir l'accuser.
Waɗansu daga cikin mutane suna neman dalilin zargin Yesu, sai suka zuba masa ido, su ga ko zai warkar da shi a ranar Asabbaci.
3 Il dit à l'homme qui avait la main desséchée: Lève-toi et tiens-toi au milieu de nous.
Yesu ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.”
4 Puis il leur dit: Est-il permis, le jour du sabbat, de faire du bien ou de faire du mal; de sauver une personne ou de la tuer? Mais ils gardaient le silence.
Sai Yesu ya tambaye su ya ce, “Me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri, ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a yi kisa?” Amma suka yi shiru.
5 Alors, promenant sur eux ses regards avec indignation, et affligé de l'endurcissement de leur coeur, il dit à l'homme: Étends ta main. Il l'étendit, et sa main redevint saine.
Sai ya kalle su da fushi, don taurin zuciyarsu ya ɓata masa rai sosai. Sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
6 Les pharisiens, étant sortis, tinrent aussitôt conseil avec les hérodiens contre lui, pour le faire périr.
Sai Farisiyawa suka fita, suka fara ƙulla shawara da mutanen Hiridus yadda za su kashe Yesu.
7 Jésus se retira avec ses disciples du côté de la mer, et une grande multitude, venue de la Galilée, le suivit. De la Judée aussi,
Yesu da almajiransa suka janye zuwa tafkin, taro mai yawa kuwa daga Galili ya bi shi.
8 de Jérusalem, de l'Idumée, du pays au-delà du Jourdain, ainsi que des environs de Tyr et de Sidon, une grande multitude, ayant entendu parler de tout ce qu'il faisait, vint vers lui.
Mutane da yawa daga Yahudiya, da Urushalima, da Edom, da kuma yankunan da suke ƙetaren Urdun, da kewayen Taya, da Sidon suka zo wurinsa, don sun ji dukan abubuwan da yake yi.
9 Alors il dit à ses disciples de lui tenir une petite barque toute prête, à cause de la foule, pour ne pas être trop pressé par elle.
Saboda taron, sai ya ce wa almajiransa su shirya masa ƙaramin jirgin ruwa, don kada mutane su matse shi.
10 Car il avait guéri plusieurs malades, de sorte que tous ceux qui avaient quelque mal se jetaient sur lui pour le toucher.
Gama ya warkar da mutane da yawa, masu cututtuka suka yi ta ƙoƙarin zuwa gaba, don su taɓa shi.
11 Et quand les esprits impurs le voyaient, ils tombaient à ses pieds et s'écriaient: Tu es le Fils de Dieu!
Duk sa’ad da mugayen ruhohi suka gan shi, sai fāɗi a gabansa, su ɗaga murya, su ce, “Kai Ɗan Allah ne.”
12 Mais il leur défendait sévèrement de le faire connaître.
Amma yakan tsawata musu, kada su shaida ko wane ne shi.
13 Il alla ensuite sur la montagne, et il appela ceux qu'il voulut choisir lui-même, et ils vinrent à lui.
Yesu ya hau gefen wani dutse, ya kira waɗanda yake so, suka kuma zo wurinsa.
14 Il en désigna douze, qu'il nomma apôtres, pour les avoir avec lui et pour les envoyer prêcher,
Ya naɗa sha biyu, ya kira su manzanni don su kasance tare da shi, domin kuma yă aike su yin wa’azi,
15 avec le pouvoir de chasser les démons.
don kuma su sami ikon fitar da aljanu.
16 Voici les douze qu'il désigna: Simon, à qui il donna le nom de Pierre;
Ga sha biyun da ya naɗa. Siman (wanda ya ba shi suna Bitrus);
17 Jacques, fils de Zébédée, et Jean, frère de Jacques, auxquels il donna le nom de Boanerges, c'est-à-dire fils du tonnerre;
Yaƙub ɗan Zebedi da kuma ɗan’uwansa Yohanna (ga waɗannan kuwa ya sa musu suna Buwarnajis, wato, “’ya’yan tsawa”);
18 André, Philippe, Barthélémy, Matthieu, Thomas, Jacques, fils d'Alphée, Thaddée, Simon le Cananéen,
Andarawus, Filibus, Bartolomeyu, Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Taddayus, Siman wanda ake kira Zilot,
19 et Judas Iscariote, celui-là même qui le trahit.
da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
20 Jésus entra dans une maison avec ses disciples; et la foule s'y rassembla encore, de sorte qu'ils ne pouvaient pas même prendre leur repas.
Sai Yesu ya shiga wani gida, taro kuma ya sāke haɗuwa, har shi da almajiransa ma ba su sami damar cin abinci ba.
21 Quand ses proches l'eurent appris, ils vinrent pour s'emparer de lui; car ils disaient qu'il avait perdu l'esprit.
Da’yan’uwansa suka sami wannan labari, sai suka tafi don su dawo da shi, suna cewa, “Ai, ya haukace.”
22 Les scribes, descendus de Jérusalem, disaient: Il est possédé de Béelzébul, et il chasse les démons par le prince des démons!
Malaman dokokin da suka zo daga Urushalima suka ce, “Ai, yana da Be’elzebub! Da ikon sarkin aljanu yake fitar da aljanu.”
23 Mais Jésus, les ayant appelés, leur dit en paraboles: Comment Satan pourrait-il chasser Satan?
Sai Yesu ya kira su, ya yi musu magana da misalai ya ce, “Yaya Shaiɗan zai fitar da Shaiɗan?
24 Si un royaume est divisé contre lui-même, ce royaume-là ne peut subsister;
In mulki yana gāba da kansa, wannan mulki ba zai tsaya ba.
25 et si une maison est divisée contre elle-même, cette maison-là ne saurait subsister.
In gida yana gāba da kansa, wannan gida ba zai tsaya ba.
26 Si donc Satan s'élève contre lui-même, il est divisé et il ne peut subsister, mais il est près de sa fin.
In kuwa Shaiɗan yana gāba da kansa, ya kuma rabu biyu, ba zai tsaya ba, ƙarshensa ya zo ke nan.
27 Nul ne peut entrer dans la maison de l'homme fort et piller son bien, s'il n'a auparavant lié cet homme fort; après cela, il pourra piller sa maison.
Tabbatacce, ba mai shiga gidan mai ƙarfi yă kwashe dukiyarsa, sai bayan ya daure mai ƙarfin, sa’an nan zai iya yin fashin gidansa.
28 En vérité, je vous le dis, tous les péchés seront pardonnés aux enfants des hommes, ainsi que tous les blasphèmes qu'ils auront proférés;
Gaskiya nake gaya muku, za a gafarta duk zunubai da kuma saɓon mutane suka yi.
29 mais tout homme qui aura blasphémé contre le Saint-Esprit, n'en obtiendra jamais le pardon; il est coupable d'un péché éternel. (aiōn g165, aiōnios g166)
Amma duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a taɓa gafara masa ba. Ya aikata madawwamin zunubi ke nan.” (aiōn g165, aiōnios g166)
30 Jésus parla ainsi, parce qu'ils disaient: Il est possédé d'un esprit impur.
Ya faɗi haka domin suna cewa, “Yana da mugun ruhu.”
31 La mère et les frères de Jésus arrivèrent; et, se tenant dehors, ils l'envoyèrent appeler.
Sai mahaifiyar Yesu tare da’yan’uwansa suka iso. Suna tsaye a waje, sai suka aiki wani ciki yă kira shi.
32 La foule était assise autour de lui. Et on lui dit: Voici que ta mère et tes frères sont là dehors, qui te cherchent.
Taron yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Mahaifiyarka da’yan’uwanka suna waje, suna nemanka.”
33 Mais il répondit: Qui est ma mère, et qui sont mes frères?
Ya yi tambaya ya ce, “Su wane ne mahaifiyata, da’yan’uwana?”
34 Puis, jetant les yeux sur ceux qui étaient assis autour de lui, il dit: Voilà ma mère et mes frères!
Sai ya dubi waɗanda suke zaune kewaye da shi ya ce, “Ga mahaifiyata da’yan’uwana!
35 Quiconque fait la volonté de Dieu, celui-là est mon frère, et ma soeur, et ma mère.
Duk wanda yake aikata nufin Allah, shi ne ɗan’uwana, da’yar’uwata, da kuma mahaifiyata.”

< Marc 3 >