< Luc 1 >

1 Plusieurs ayant entrepris d'écrire l'histoire des faits accomplis parmi nous,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 — tels que nous les ont transmis ceux qui en ont été, dès le commencement, les témoins oculaires, et qui sont devenus ministres de la Parole,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 — j'ai cru bon, moi aussi, très excellent Théophile, de te les exposer par écrit et dans leur ordre, après m'être exactement informé de tout, depuis l'origine,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 afin que tu reconnaisses la solidité des enseignements que tu as reçus.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Au temps d'Hérode, roi de Judée, il y avait un sacrificateur nommé Zacharie, de la classe d'Abia; sa femme était de la race d'Aaron et s'appelait Élisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ils étaient tous deux justes devant Dieu, et ils suivaient tous les commandements et toutes les prescriptions du Seigneur d'une manière irréprochable.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Ils n'avaient point d'enfants, parce qu'Elisabeth était stérile; et ils étaient tous deux avancés en âge.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Or, il arriva, comme Zacharie remplissait devant Dieu les fonctions du sacerdoce, suivant le rang de sa classe,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 qu'il fut appelé par le sort, d'après la coutume établie parmi les sacrificateurs, à entrer dans le sanctuaire du Seigneur pour y offrir le parfum.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Toute la multitude du peuple était dehors en prière, à l'heure où le parfum était offert.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Alors un ange du Seigneur lui apparut, debout à droite de l'autel des parfums.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zacharie, en le voyant, fut troublé, et la frayeur le saisit.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Mais l'ange lui dit: Ne crains point, Zacharie; car ta prière a été exaucée. Elisabeth, ta femme, t'enfantera un fils, et tu lui donneras le nom de Jean.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Il sera pour toi un sujet de joie et d'allégresse, et plusieurs se réjouiront de sa naissance.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 En effet, il sera grand devant le Seigneur; il ne boira ni vin ni cervoise, et il sera rempli du Saint-Esprit dès le sein de sa mère.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Il convertira plusieurs des fils d'Israël au Seigneur, leur Dieu;
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 et lui-même marchera devant le Seigneur, dans l'esprit et avec la puissance d'Élie, pour ramener les coeurs des pères vers les enfants, et les rebelles à la sagesse des justes, afin de préparer au Seigneur un peuple bien disposé.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zacharie dit à l'ange: A quoi reconnaîtrai-je cela? Car je suis vieux, et ma femme est avancée en âge.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 L'ange lui répondit: Je suis Gabriel, qui me tiens devant Dieu; j'ai été envoyé pour te parler et t'annoncer cette bonne nouvelle.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Voici que tu vas devenir muet, et tu ne pourras parler jusqu'au jour où ces choses arriveront, parce que tu n'as pas cru à mes paroles, qui s'accompliront en leur temps.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Cependant, le peuple attendait Zacharie, et s'étonnait de ce qu'il s'attardait dans le sanctuaire.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Quand il sortit, Zacharie ne pouvait leur parler; et ils comprirent qu'il avait eu quelque vision dans le sanctuaire; il leur faisait des signes, et il demeura muet.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Lorsque les jours de son ministère furent achevés, il retourna dans sa maison.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Quelque temps après, Elisabeth sa femme, devint enceinte; elle se tint cachée durant cinq mois, et elle disait:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Voilà ce que le Seigneur m'a fait, quand il a jeté les yeux sur moi, pour ôter l'opprobre qui pesait sur moi parmi les hommes.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Au sixième mois. Dieu envoya l'ange Gabriel dans une ville de Galilée, appelée Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 auprès d'une vierge fiancée à un homme nommé Joseph, de la maison de David; cette vierge s'appelait Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 L'ange, étant entré dans le lieu où elle était, lui dit: Je te salue, toi qui as été comblée de grâces; le Seigneur est avec toi.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Elle fut troublée de ces paroles, et elle se demandait ce que signifiait cette salutation.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Alors l'ange lui dit: Ne crains point, Marie; car tu as trouvé grâce devant Dieu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Voici que tu enfanteras et mettras au monde un fils, à qui tu donneras le nom de Jésus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Il sera grand, et il sera appelé le Fils du Très-Haut; et le Seigneur, Dieu, lui donnera le trône de David, son père.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 Il régnera éternellement sur la maison de Jacob, et son règne n'aura pas de fin. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Alors Marie dit à l'ange: Comment cela arrivera-t-il, puisque je ne connais point d'homme?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 L'ange lui répondit: L'Esprit saint viendra sur toi, et la puissance du Très-Haut te couvrira de son ombre; c'est pourquoi aussi, le saint enfant qui naîtra sera appelé le Fils de Dieu.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Et voici qu'Elisabeth, ta parente, a aussi conçu un fils en sa vieillesse; c'est ici le sixième mois de celle qui était appelée stérile.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Car rien n'est impossible à Dieu!
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Marie répondit: Me voici: je suis la servante du Seigneur. Qu'il me soit fait selon ta parole! Puis l'ange la quitta.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 En ces jours-là, Marie, s'étant levée, s'empressa d'aller dans le pays des montagnes, dans, une ville de Juda.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Elle entra dans la maison de Zacharie, et salua Elisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Or il arriva, quand Elisabeth eut entendu la salutation de Marie, que le petit enfant tressaillit dans son sein; et Elisabeth fut remplie du Saint-Esprit.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Alors élevant la voix, elle s'écria: Tu es bénie entre les femmes, et le fruit de tes entrailles est béni.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Et d'où me vient cet honneur, que la mère de mon Seigneur vienne me visiter?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Car ta voix, quand tu m'as saluée, n'a pas plus tôt frappé mes oreilles, que le petit enfant a tressailli de joie dans mon sein.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Bienheureuse est celle qui a cru; car ce qui lui a été dit de la part du Seigneur aura son accomplissement!
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Alors Marie dit: Mon âme magnifie le Seigneur,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 et mon esprit se réjouit en Dieu, qui est mon Sauveur,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 parce qu'il a jeté les yeux sur la bassesse de sa servante. Et voici que désormais tous les âges m'appelleront bienheureuse;
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 car le Tout-Puissant a fait pour moi de grandes choses. Son nom est saint,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 et sa miséricorde s'étend d'âge en âge sur ceux qui le craignent.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Il a manifesté la vigueur de son bras. Il a dissipé les desseins que les orgueilleux formaient dans leur coeur.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Il a renversé de leurs trônes les puissants, et il a élevé les humbles.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Il a comblé de biens les affamés, et il a renvoyé les riches les mains vides.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Il est venu au secours d'Israël, son serviteur, et il s'est souvenu de sa miséricorde
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 — ainsi qu'il en avait parlé à nos pères — à l'égard d'Abraham et de sa postérité, pour toujours. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Marie demeura avec Elisabeth environ trois mois; puis elle s'en retourna dans sa maison.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Cependant, le terme d'Elisabeth étant venu, elle enfanta un fils.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Ses voisins et ses parents, ayant appris que le Seigneur avait fait éclater en elle la grandeur de sa miséricorde, s'en réjouissaient avec elle.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Le huitième jour, ils vinrent pour circoncire l'enfant; ils l'appelaient Zacharie, du nom de son père.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Mais sa mère dit: Non! Il sera nommé Jean.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Ils lui dirent: Il n'y a personne dans ta famille qui soit appelé de ce nom.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Alors ils demandèrent au père, par signes, comment il voulait que l'enfant fût nommé.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Zacharie ayant demandé des tablettes, écrivit: Jean est son nom. Et ils furent tous surpris.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 A l'instant sa bouche s'ouvrit, sa langue se délia, et il parlait, bénissant Dieu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Tous leurs voisins furent remplis de crainte, et l'on s'entretenait de toutes ces choses dans tout le pays des montagnes de la Judée.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Tous ceux qui les entendirent les conservèrent dans leur coeur et ils disaient: Que deviendra donc ce petit enfant? Car la main du Seigneur était avec lui.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Alors Zacharie, son père, fut rempli de l'Esprit saint. Il prophétisa et il dit:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Béni soit le Seigneur, le Dieu d'Israël, de ce qu'il a visité et racheté son peuple,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 et nous a suscité un puissant Sauveur dans la maison de David, son serviteur,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 comme il l'avait proclamé par la bouche de ses saints prophètes, dès les anciens temps. (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Il nous délivre de nos ennemis et de la main de tous ceux qui nous haïssent.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Il exerce sa miséricorde envers nos pères et se souvient de sa sainte alliance;
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 car il a fait à Abraham, notre père, le serment de nous accorder cette grâce,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 qu'après avoir été délivrés de la main de nos ennemis, nous pourrions le servir sans crainte,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 en sa présence, dans la sainteté et la justice, tous les jours de notre vie.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Et toi, petit enfant, tu seras appelé le prophète du Très-Haut; car tu marcheras devant la face du Seigneur, pour préparer ses voies,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 pour donner à son peuple la connaissance du salut par la rémission de ses péchés.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Les entrailles de la miséricorde de notre Dieu se sont émues, et le soleil levant nous a visités d'en haut,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 pour éclairer ceux qui sont assis dans les ténèbres et l'ombre de la mort, et pour conduire nos pas dans le chemin de la paix.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Or, le petit enfant grandissait et se fortifiait en esprit; et il demeura dans les déserts jusqu'au jour de sa manifestation à Israël.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luc 1 >