< Luc 1 >

1 Cher Théophile, puisque plusieurs autres ont essayé de rédiger un récit des faits accomplis parmi nous,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 tels que nous les ont transmis ceux qui en ont été, dès l’origine, témoins oculaires et qui sont devenus ministres de la Parole,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 j’ai cru devoir, moi aussi, après m’être soigneusement informé de tout, depuis le commencement, t’en écrire une narration suivie,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 pour que tu reconnaisses la solidité des enseignements que tu as reçus.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Aux jours d'Hérode, roi de Judée, vivait un prêtre nommé Zaccharie. Il était de la classe d'Abia et sa femme était d'entre les filles d'Aaron. Son nom était Élisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Tous deux étaient justes devant Dieu, marchant irréprochables dans tous les commandements et toutes les ordonnances du Seigneur.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Ils n'avaient point d'enfants; parce qu'Élisabeth était stérile; et tous deux étaient avancés en âge.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Or, le tour de sa classe étant venu de remplir devant Dieu les fonctions sacerdotales,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 il lui échut par le sort (qui était le mode usité entre les prêtres) d'entrer dans le sanctuaire du Seigneur pour y offrir l'encens.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Pendant cette heure de l'encens, la foule du peuple restait au dehors et priait.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Or, à la droite de l'autel de l'encens, apparut à Zaccharie un ange du Seigneur, debout devant lui.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 A sa vue Zaccharie fut troublé, et la crainte le saisit.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 «Ne crains point, Zaccharie, lui dit l'ange; car ta prière a été exaucée et ta femme Élisabeth t'enfantera un fils; tu lui donneras le nom de Jean.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Il sera ta joie et ton allégresse, et beaucoup se réjouiront de sa naissance. Devant le Seigneur,
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 en effet, il sera grand; il ne devra jamais boire ni vin, ni cervoise; et, tout rempli de l'Esprit saint dès les entrailles de sa mère,
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 il ramènera au Seigneur leur Dieu, de nombreux enfants d'Israël.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Lui-même, dans l'esprit et la vertu d'Élie, se mettra en marche devant le Seigneur, afin de faire revivre dans les enfants le coeur même des aïeux, de ramener les rebelles à la sagesse des justes, et de préparer au Seigneur un peuple bien disposé.» —
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 «A quoi reconnaîtrai-je cela, dit à l'ange Zaccharie, car je suis moi-même un vieillard, et ma femme est avancée en âge.»
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 L'ange lui répondit par ces paroles: «Je suis, Gabriel qui me tiens devant Dieu. Et j'ai été envoyé pour te parler et t'annoncer cette Bonne Nouvelle.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Et à cause de ton manque de foi en mes paroles, qui s'accompliront en leur temps, voilà que tu seras muet et ne pourras parler jusqu'au jour où ces choses arriveront.»
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Le peuple cependant attendait Zaccharie, et s'étonnait de le voir s'attarder dans le sanctuaire.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Lorsqu'il sortit, il lui fut impossible de leur parler; on comprit qu'il avait eu une vision dans le sanctuaire. Lui-même le leur faisait entendre par signes. Zaccharie resta sourd-muet.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Quand la période de ses fonctions fut terminée, il retourna en sa maison;
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 ce fut alors que sa femme Élisabeth devint enceinte. Pendant cinq mois elle vécut dans le secret de sa demeure.
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 «Voilà, disait-elle, ce qu'a fait pour moi le Seigneur en ces jours où il m'a regardée pour mettre fin à mon opprobre parmi les hommes.»
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Le sixième mois, Dieu envoya l'ange Gabriel dans une ville de Galilée, appelée Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 vers une vierge, fiancée à un homme de la famille de David, nommé Joseph. Le nom de la vierge était Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 L'ange, étant entré où elle était, lui dit: «Salut! une grâce, t'a été faite; le Seigneur est avec toi!»
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 A ces paroles, Marie fut toute troublée; et elle se demandait ce que pouvait être une semblable salutation.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 «Ne crains point, Marie, reprit l'ange, car tu as trouvé grâce près de Dieu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Sache que tu vas concevoir en ton sein et enfanter un fils auquel tu donneras le nom de Jésus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Il sera grand; on l'appellera: Fils du Très-Haut; à lui le Seigneur Dieu donnera le trône de David son père;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 il régnera à jamais sur la maison de Jacob et son règne n'aura point de fin.» (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Alors Marie dit à l'ange: «Comment cela se fera-t-il, puisque je ne connais point, d’homme?»
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Et l'ange lui répondit par ces paroles: «L'Esprit saint viendra sur toi, et une puissance du Très-Haut t'enveloppera de son ombre. C'est pourquoi l'Être saint qui doit naître sera appelé Fils de Dieu!
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Sache également qu'en sa vieillesse, ta parente Élisabeth, elle aussi, a conçu un fils, et que celle que l'on appelait stérile en est déjà à son sixième mois.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Rien n'est impossible à Dieu.»
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Alors Marie dit: «Voici la servante du Seigneur. Qu'il me soit fait suivant ta parole.» Et l'ange la quitta.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 En ces jours-là, Marie se hâta de partir, se dirigeant vers le pays des montagnes. Elle alla dans une ville de Juda.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 En entrant dans la maison de Zaccharie elle salua Élisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Et dès qu'Élisabeth eut entendu la salutation de Marie, l'enfant qu'elle portait tressaillit, et elle-même fut remplie d'Esprit saint.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 «Tu es bénie entre les femmes, s'écria-t-elle en élevant la voix, et le fruit de tes entrailles est béni!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 D'où me vient que la mère de mon Seigneur vienne me visiter?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Aussitôt que ta voix, quand tu m'as saluée, a frappé mon oreille, l'enfant a tressailli de joie dans mon sein.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Bienheureuse celle qui a cru à l'accomplissement de ce qui lui a été dit de la part du Seigneur!»
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Et Marie dit: «Mon âme magnifie le Seigneur,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Et mon esprit est transporté de joie en Dieu mon Sauveur,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Parce qu'il a abaissé son regard sur l'humilité de sa servante. Voilà que désormais toutes les générations m'appelleront la bienheureuse,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Parce que le Tout-Puissant m'a fait de grandes choses! Son nom est saint,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Sa miséricorde se répand de génération en génération Sur ceux qui le craignent.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Il a déployé la force de son bras, Il a dissipé les pensées des coeurs des superbes,
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Il a jeté bas de leurs trônes les puissants, Et il a exalté les humbles;
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Il a comblé de biens les affamés, Et il a renvoyé les riches à vide;
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Il a secouru Israël son serviteur, Il s'est souvenu de sa miséricorde,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 Ainsi qu'il l'avait dit à nos pères, à Abraham et à sa postérité pour toujours.» (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Marie séjourna environ trois mois avec Élisabeth, et retourna ensuite en sa maison.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Parvenue au terme de sa grossesse, Élisabeth enfanta un fils.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Ayant appris que le Seigneur faisait ainsi éclater par elle sa miséricorde, ses voisins et ses parents partagèrent sa joie.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Le huitième jour, ils vinrent pour la circoncision de l'enfant. Ils lui donnaient le nom de Zaccharie, celui de son père,
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 quand sa mère prit la parole: «Non, dit-elle, il se nommera Jean.» —
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 «Mais, lui dirent les autres, personne dans ta famille ne porte ce nom.»
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Et l'on demanda au père, par signes, comment il voulait le nommer.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Alors, se faisant apporter des tablettes, Zaccharie écrivit ceci: «Jean est son nom.» Tout le monde fut surpris.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Aussitôt la banche de Zaccharie s'ouvrit, sa langue se délia et il se mit à parler et à bénir Dieu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Chacun dans le voisinage fut saisi de crainte et, dans la région des montagnes de Judée, il ne fut bruit que de toutes ces choses.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Chacun en les apprenant les recueillait dans son coeur et disait: «Que sera donc cet enfant?» En effet, la main du Seigneur était avec lui.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Quant à Zaccharie, son père, il fut rempli d'Esprit saint et il prophétisa en ces termes:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 «Béni soit le Seigneur, le Dieu d'Israël! Car il a visité son peuple et opéré sa rédemption;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Il nous a suscité un Sauveur puissant, De la maison de David, son serviteur.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 (Ainsi qu'il l'avait annoncé par la bouche de ses saints prophètes qui jadis ont vécu.) (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Il nous délivre de nos ennemis, Et de la main de tous ceux qui nous haïssent;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Il montre sa miséricorde envers nos pères; Il se souvient de sa sainte alliance;
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Du serment par lui juré à notre père Abraham; Il nous donne enfin à nous,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 délivrés de la main de nos ennemis, De le servir sans crainte, [de notre vie;
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 De marcher devant lui dans la sainteté et la justice tous les jours
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Et toi, enfant, tu seras appelé Prophète du Très-Haut; Car tu iras devant le Seigneur; Tu marcheras devant lui pour lui préparer les voies;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Tu donneras à son peuple la science du salut, Tu lui diras que ses péchés lui sont remis;
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Que notre Dieu a des entrailles de miséricorde, Qu'il nous a regardés du haut des cieux, Que le soleil d'Orient se lève;
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Qu'il illuminera ceux qui sont assis dans les ténèbres et l'ombre de la mort; Qu'il dirigera nos pas dans un chemin de paix.»
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 L'enfant grandissait et son esprit se fortifiait, et jusqu'au jour de sa manifestation à Israël, les déserts furent sa demeure.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luc 1 >