< Luc 8 >

1 Ensuite, Jésus allait de ville en ville, et de village en village, prêchant et annonçant la bonne nouvelle du royaume de Dieu; et les douze étaient avec lui,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 Ainsi que quelques femmes qui avaient été délivrées d'esprits malins et de maladies; savoir, Marie appelée Magdelène, de laquelle il était sorti sept démons;
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 Et Jeanne, femme de Chouza, intendant d'Hérode, et Suzanne, et plusieurs autres, qui l'assistaient de leurs biens.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Or, comme une grande foule de peuple s'assemblait, et que plusieurs venaient à lui de toutes les villes, il leur dit en parabole:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 Un semeur sortit pour semer sa semence, et en semant, une partie du grain tomba le long du chemin, et elle fut foulée, et les oiseaux du ciel la mangèrent toute.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Et une autre partie tomba sur un endroit pierreux; et quand elle fut levée, elle sécha, parce qu'elle n'avait point d'humidité.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Et une autre partie tomba parmi les épines, et les épines levèrent avec le grain, et l'étouffèrent.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 Et une autre partie tomba dans une bonne terre; et étant levée, elle rendit du fruit, cent pour un. En disant ces choses, il criait: Que celui qui a des oreilles pour entendre, entende!
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Ses disciples lui demandèrent ce que signifiait cette parabole.
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 Et il répondit: Il vous a été donné de connaître les mystères du royaume de Dieu; mais il en est parlé aux autres en paraboles, de sorte qu'en voyant ils ne voient point, et qu'en entendant ils ne comprennent point.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Voici ce que cette parabole signifie.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 La semence, c'est la parole de Dieu; ceux qui la reçoivent le long du chemin sont ceux qui l'écoutent; mais le diable vient, qui ôte cette parole de leur cœur, de peur qu'en croyant, ils ne soient sauvés;
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Ceux qui la reçoivent dans des endroits pierreux sont ceux qui ayant entendu la parole, la reçoivent avec joie, mais ils n'ont point de racine, et ils ne croient que pour un temps; et quand la tentation survient, ils se retirent;
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Et ce qui est tombé parmi les épines, ce sont ceux qui ont entendu la parole; mais qui, s'en allant, la laissent étouffer par les inquiétudes, par les richesses et par les voluptés de cette vie, de sorte qu'ils ne portent point de fruit qui vienne à maturité;
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Mais ce qui est tombé dans une bonne terre, ce sont ceux qui, ayant entendu la parole avec un cœur honnête et bon, la retiennent et portent du fruit avec persévérance.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Personne, après avoir allumé une lampe, ne la couvre d'un vaisseau, ni ne la met sous le lit; mais il la met sur un chandelier, afin que ceux qui entrent, voient la lumière.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Car il n'y a rien de secret qui ne doive être manifesté, ni rien de caché qui ne doive être connu et venir en évidence.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Prenez donc garde à la manière dont vous écoutez; car on donnera à celui qui a, mais pour celui qui n'a pas, on lui ôtera même ce qu'il croit avoir.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Alors sa mère et ses frères vinrent le trouver; mais ils ne pouvaient l'aborder à cause de la foule.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 Et on vint lui dire: Ta mère et tes frères sont là dehors, qui désirent te voir.
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 Mais il répondit: Ma mère et mes frères sont ceux qui écoutent la parole de Dieu, et qui la mettent en pratique.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Il arriva un jour, qu'il entra dans une barque avec ses disciples, et il leur dit: Passons de l'autre côté du lac; et ils partirent.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 Et comme ils voguaient, il s'endormit; et un vent impétueux s'éleva sur le lac, la barque s'emplissait, et ils étaient en danger.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Alors ils vinrent vers lui, et le réveillèrent, en disant: Maître, Maître, nous périssons. Mais lui, étant réveillé, parla avec autorité au vent et à la tempête, qui s'apaisèrent, et le calme se rétablit.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 Alors il leur dit: Où est votre foi? Et eux, saisis de crainte et d'admiration, disaient entre eux: Qui donc est celui-ci, qui commande même aux vents et à l'eau, et ils lui obéissent.
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Ils abordèrent ensuite au pays des Gadaréniens, qui est vis-à-vis de la Galilée.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Et quand Jésus fut descendu à terre, il vint au-devant de lui un homme de cette ville-là, qui était possédé des démons depuis longtemps. Il ne portait point d'habits, et il ne demeurait point à la maison; mais il se tenait dans les sépulcres.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Dès qu'il vit Jésus, il cria, et se jetant à ses pieds, il dit à haute voix: Qu'y a-t-il entre moi et toi, Jésus, Fils du Dieu très haut? Je te prie, ne me tourmente point.
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 Car Jésus commandait à l'esprit immonde de sortir de cet homme, dont il s'était saisi depuis longtemps; on le liait de chaînes et on le gardait avec des entraves, mais il rompait ses liens, et il était emporté par le démon dans les déserts.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Et Jésus lui demanda: Comment t'appelles-tu? Et il répondit: Légion; car plusieurs démons étaient entrés en lui.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 Et ils le priaient de ne leur pas commander d'aller dans l'abîme. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Or, il y avait là un grand troupeau de pourceaux qui paissaient sur la montagne; et ils le priaient qu'il leur permît d'entrer dans ces pourceaux, et il le leur permit.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Les démons étant donc sortis de cet homme, entrèrent dans les pourceaux, et le troupeau se précipita de ce lieu escarpé dans le lac, et fut noyé.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 Et ceux qui les paissaient, voyant ce qui était arrivé, s'enfuirent et le racontèrent dans la ville et à la campagne.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Alors les gens sortirent pour voir ce qui s'était passé; et étant venus vers Jésus, ils trouvèrent l'homme duquel les démons étaient sortis, assis aux pieds de Jésus, habillé et dans son bon sens; et ils furent saisis de frayeur.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Et ceux qui avaient vu ces choses leur racontèrent comment le démoniaque avait été délivré.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Et tous ceux du pays des Gadaréniens le prièrent de se retirer de chez eux; car ils étaient saisis d'une grande crainte. Il entra donc dans la barque pour s'en retourner.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Et l'homme duquel les démons étaient sortis, le priait de lui permettre d'être avec lui; mais Jésus le renvoya, en disant:
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 Retourne dans ta maison, et raconte les grandes choses que Dieu t'a faites. Il s'en alla donc, publiant par toute la ville tout ce que Jésus avait fait en sa faveur.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Quand Jésus fut de retour, il fut reçu par une grande multitude; car tous l'attendaient.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 Et voici un homme nommé Jaïrus, qui était chef de la synagogue, vint, et se jetant aux pieds de Jésus, le pria de venir dans sa maison;
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 Parce qu'il avait une fille unique, d'environ douze ans, qui se mourait. Et comme Jésus y allait, il était pressé par la foule.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Alors une femme, qui avait une perte de sang depuis douze ans, et qui avait dépensé tout son bien en médecins, sans avoir pu être guérie par aucun,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 S'approchant de lui par-derrière, toucha le bord de son vêtement; et à l'instant, sa perte de sang s'arrêta.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 Et Jésus dit: Qui m'a touché? Et comme tous le niaient, Pierre et ceux qui étaient avec lui, dirent: Maître, la foule t'environne et te presse; et tu dis: Qui m'a touché?
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 Mais Jésus dit: Quelqu'un m'a touché; car j'ai senti qu'une vertu est sortie de moi.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 Cette femme voyant que cela ne lui avait point été caché, vint toute tremblante, et se jetant à ses pieds, elle déclara, devant tout le peuple, pour quel sujet elle l'avait touché, et comment elle avait été guérie à l'instant.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Et Jésus lui dit: Ma fille, rassure-toi, ta foi t'a guérie; va-t'en en paix.
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 Comme il parlait encore, quelqu'un vint de chez le chef de la synagogue, qui lui dit: Ta fille est morte; ne fatigue pas le Maître.
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Mais Jésus, l'ayant entendu, dit à Jaïrus: Ne crains point; crois seulement, et elle sera guérie.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 Et quand il fut arrivé dans la maison, il ne laissa entrer personne que Pierre, Jacques et Jean, et le père et la mère de la fille.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Et tous pleuraient et se lamentaient à cause d'elle; mais il dit: Ne pleurez point; elle n'est pas morte, mais elle dort.
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 Et ils se moquaient de lui, sachant qu'elle était morte.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 Mais, les ayant tous fait sortir, il la prit par la main, et il cria: Enfant, lève-toi.
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Et son esprit revint; elle se leva à l'instant, et il commanda qu'on lui donnât à manger.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Et ses parents furent tout étonnés; mais il leur défendit de dire à personne ce qui était arrivé.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luc 8 >