< Luc 5 >

1 Comme Jésus était sur le bord du lac de Génézareth, la foule se jetait sur lui pour entendre la parole de Dieu.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Et ayant vu, au bord du lac, deux barques, dont les pêcheurs étaient descendus et lavaient leurs filets, il monta dans l'une de ces barques, qui était à Simon,
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Et il le pria de s'éloigner un peu du rivage; et s'étant assis, il enseignait le peuple de dessus la barque.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Et quand il eut cessé de parler, il dit à Simon: Avance en pleine eau, et jetez vos filets pour pêcher.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Simon lui répondit: Maître, nous avons travaillé toute la nuit sans rien prendre; toutefois, sur ta parole, je jetterai le filet.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Et l'ayant fait, ils prirent une grande quantité de poissons;
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Et comme leur filet se rompait, ils firent signe à leurs compagnons, qui étaient dans l'autre barque, de venir les aider; ils y vinrent, et ils remplirent les deux barques, tellement qu'elles s'enfonçaient.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Simon Pierre, ayant vu cela, se jeta aux pieds de Jésus et lui dit: Seigneur, retire-toi de moi; car je suis un homme pécheur.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Car la frayeur l'avait saisi, et tous ceux qui étaient avec lui, à cause de la pêche des poissons qu'ils avaient faite; de même que Jacques et Jean, fils de Zébédée, qui étaient compagnons de Simon.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Et Jésus dit à Simon: N'aie point de peur; désormais tu seras pêcheur d'hommes vivants.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Et ayant ramené leurs barques à bord, ils abandonnèrent tout et le suivirent.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Comme il était dans une des villes de la Galilée, un homme tout couvert de lèpre, ayant vu Jésus, se jeta la face contre terre, et le pria, disant: Seigneur, si tu le veux, tu peux me nettoyer.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Et Jésus étendit la main, le toucha et lui dit: Je le veux, sois nettoyé. Et au même instant la lèpre le quitta.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Et Jésus lui défendit de le dire à personne; mais va, lui dit-il, montre-toi au sacrificateur, et offre pour ta purification ce que Moïse a commandé, afin que cela leur serve de témoignage.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Et sa réputation se répandait de plus en plus, et une foule de gens s'assemblaient pour l'entendre et pour être guéris par lui de leurs maladies.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Mais il se tenait retiré dans les déserts, et il priait.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Or, un jour qu'il enseignait, et que des pharisiens et des docteurs de la loi, qui étaient venus de tous les bourgs de la Galilée et de la Judée, et de Jérusalem, étaient là assis, la puissance du Seigneur agissait pour guérir les malades.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Alors il survint des gens qui portaient sur un lit un homme perclus, et ils cherchaient à le faire entrer dans la maison et à le mettre devant Jésus.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Et ne sachant par où le faire entrer à cause de la foule, ils montèrent sur la maison, et le descendirent par les tuiles avec son lit, au milieu de la foule,
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Devant Jésus, qui, ayant vu leur foi, lui dit: O homme, tes péchés te sont pardonnés.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Alors les scribes et les pharisiens commencèrent à raisonner et à dire: Qui est celui-ci, qui prononce des blasphèmes? Qui peut pardonner les péchés, que Dieu seul?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Mais Jésus, connaissant leurs pensées, prit la parole et leur dit: Quel raisonnement faites-vous dans vos cœurs?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Lequel est le plus aisé, de dire: Tes péchés te sont pardonnés; ou de dire: Lève-toi, et marche?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Or, afin que vous sachiez que le Fils de l'homme a sur la terre le pouvoir de pardonner les péchés: Lève-toi, dit-il au paralytique, je te le dis, emporte ton lit, et t'en va dans ta maison.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Et à l'instant il se leva en leur présence; il emporta le lit sur lequel il avait été couché, et s'en alla dans sa maison, donnant gloire à Dieu.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Et ils furent tous saisis d'étonnement, et ils glorifiaient Dieu; ils furent remplis de crainte, et ils disaient: Nous avons vu aujourd'hui des choses étranges.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Après cela il sortit, et il vit un péager nommé Lévi, assis au bureau des impôts;
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Et il lui dit: Suis-moi. Et lui, quittant tout, se leva et le suivit.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Et Lévi lui fit un grand festin dans sa maison, et un grand nombre de péagers et d'autres gens étaient à table avec eux.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Et ceux d'entre eux qui étaient scribes et pharisiens murmuraient et disaient à ses disciples: Pourquoi mangez-vous et buvez-vous avec des péagers et des gens de mauvaise vie?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Et Jésus, prenant la parole, leur dit: Ce ne sont pas ceux qui sont en santé qui ont besoin de médecin;
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Mais ceux qui se portent mal. Je suis venu appeler à la repentance, non les justes, mais les pécheurs.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Ils lui dirent aussi: Pourquoi les disciples de Jean jeûnent-ils souvent et font-ils des prières, de même que ceux des pharisiens; au lieu que les tiens mangent et boivent?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Il leur dit: Pouvez-vous faire jeûner les amis de l'époux, pendant que l'époux est avec eux?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Mais des jours viendront où l'époux leur sera ôté; alors ils jeûneront en ces jours.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Il leur dit aussi une parabole: Personne ne met une pièce d'un habit neuf à un vieil habit; autrement, le neuf déchire le vieux, et la pièce prise du neuf ne s'accorde pas avec le vieux.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Personne non plus ne met le vin nouveau dans de vieux vaisseaux; autrement le vin nouveau romprait les vaisseaux, et se répandrait, et les vaisseaux seraient perdus.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Mais le vin nouveau se met dans des vaisseaux neufs, et les deux se conservent ensemble.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Et il n'y a personne qui, buvant du vin vieux, en veuille aussitôt du nouveau; car, dit-il, le vieux est meilleur.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luc 5 >