< Luc 1 >

1 Plusieurs ayant entrepris d'écrire l'histoire des choses dont la vérité a été pleinement établie parmi nous;
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Selon que nous les ont transmises ceux qui dès le commencement les ont vues eux-mêmes, et qui ont été les ministres de la Parole;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 J'ai cru aussi, très excellent Théophile, que je devais te les écrire par ordre, moi qui les ai toutes examinées avec soin;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Afin que tu reconnaisses la certitude des choses dont tu as été instruit.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Au temps d'Hérode, roi de Judée, il y avait un sacrificateur nommé Zacharie, du rang d'Abia; sa femme était de la race d'Aaron, et elle s'appelait Élisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ils étaient tous deux justes devant Dieu, et ils suivaient tous les commandements et toutes les ordonnances du Seigneur, d'une manière irréprochable.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Ils n'avaient point d'enfants, parce qu'Élisabeth était stérile, et qu'ils étaient tous deux avancés en âge.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Or, il arriva comme Zacharie faisait les fonctions de sacrificateur devant Dieu, selon l'ordre de son rang,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Qu'il lui échut par le sort, selon la coutume de la sacrificature, d'entrer dans le temple du Seigneur, pour y offrir les parfums.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Et toute la multitude du peuple était dehors en prières, à l'heure des parfums.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Alors un ange du Seigneur lui apparut, se tenant debout au côté droit de l'autel des parfums.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Et Zacharie le voyant, fut troublé, et la frayeur le saisit.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Mais l'ange lui dit: Zacharie, ne crains point; car ta prière est exaucée, et Élisabeth ta femme t'enfantera un fils, et tu lui donneras le nom de Jean.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Il sera pour toi un sujet de joie et de ravissement, et plusieurs se réjouiront de sa naissance.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Car il sera grand devant le Seigneur; il ne boira ni vin, ni boisson forte, et il sera rempli du Saint-Esprit dès le sein de sa mère;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Il convertira plusieurs des enfants d'Israël au Seigneur leur Dieu,
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Et il marchera devant lui dans l'esprit et avec la vertu d'Élie, pour tourner les cœurs des pères vers les enfants, et les rebelles à la sagesse des justes, afin de préparer au Seigneur un peuple bien disposé.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Et Zacharie dit à l'ange: A quoi connaîtrai-je cela? Car je suis vieux, et ma femme est avancée en âge?
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Et l'ange lui répondit: Je suis Gabriel, qui assiste devant Dieu; et j'ai été envoyé pour te parler et t'annoncer ces bonnes nouvelles.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Et voici, tu vas devenir muet, et tu ne pourras parler jusqu'au jour où ces choses arriveront, parce que tu n'as pas cru à mes paroles, qui s'accompliront en leur temps.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Cependant, le peuple attendait Zacharie, et s'étonnait de ce qu'il tardait si longtemps dans le temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Et quand il fut sorti, il ne pouvait leur parler, et ils connurent qu'il avait eu une vision dans le temple, parce qu'il le leur faisait entendre par des signes; et il demeura muet.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Et lorsque les jours de son ministère furent achevés, il s'en alla en sa maison.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Quelque temps après, Élisabeth sa femme conçut; elle se cacha durant cinq mois, et disait:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 C'est là ce que le Seigneur a fait en ma faveur, au jour où il a jeté les yeux sur moi, pour ôter mon opprobre du milieu des hommes.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Or, au sixième mois, Dieu envoya l'ange Gabriel dans une ville de Galilée,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 appelée Nazareth, à une vierge fiancée à un homme nommé Joseph, de la maison de David; et cette vierge s'appelait Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Et l'ange étant entré auprès d'elle, lui dit: Je te salue, toi qui as été reçue en grâce; le Seigneur est avec toi; tu es bénie entre les femmes.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Et ayant vu l'ange, elle fut troublée de son discours, et elle pensait en elle-même ce que pouvait être cette salutation.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Alors l'ange lui dit: Marie, ne crains point, car tu as trouvé grâce devant Dieu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Et tu concevras et tu enfanteras un fils, et tu appelleras son nom JÉSUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Il sera grand, et sera appelé Fils du Très-Haut, et le Seigneur Dieu lui donnera le trône de David son père.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 Il régnera éternellement sur la maison de Jacob, et il n'y aura point de fin à son règne. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Alors Marie dit à l'ange: Comment cela se fera-t-il, puisque je ne connais point d'homme?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Et l'ange lui répondit: Le Saint-Esprit viendra sur toi, et la puissance du Très-Haut te couvrira de son ombre; c'est pourquoi aussi le saint enfant qui naîtra de toi sera appelé le Fils de Dieu.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Et voilà, Élisabeth ta parente a aussi conçu un fils en sa vieillesse; et c'est ici le sixième mois de celle qui était appelée stérile.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Car rien n'est impossible à Dieu.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Et Marie dit: Voici la servante du Seigneur; qu'il me soit fait selon ta parole. Et l'ange se retira d'auprès d'elle.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Alors Marie se leva, et s'en alla en hâte au pays des montagnes, dans une ville de Juda.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Et étant entrée dans la maison de Zacharie, elle salua Élisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Et aussitôt qu'Élisabeth eut entendu la salutation de Marie, le petit enfant tressaillit dans son sein, et Élisabeth fut remplie du Saint-Esprit.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Et élevant la voix, elle s'écria: Tu es bénie entre les femmes, et le fruit de ton sein est béni.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Et d'où me vient ceci, que la mère de mon Seigneur vienne me visiter?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Car la voix de ta salutation n'a pas plutôt frappé mes oreilles, que le petit enfant a tressailli de joie dans mon sein.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Et heureuse est celle qui a cru; car les choses qui lui ont été dites de la part du Seigneur auront leur accomplissement.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Alors Marie dit: Mon âme magnifie le Seigneur,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Et mon esprit se réjouit en Dieu mon Sauveur;
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Parce qu'il a regardé la bassesse de sa servante. Et voici désormais tous les âges me diront bienheureuse.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Car le Tout-Puissant m'a fait de grandes choses; son nom est saint;
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Et sa miséricorde s'étend d'âge en âge sur ceux qui le craignent.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Il a déployé la force de son bras; il a dissipé les desseins que les orgueilleux formaient dans leur cœur;
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Il a détrôné les puissants, et il a élevé les petits;
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Il a rempli de biens ceux qui avaient faim, et il a renvoyé les riches à vide.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Il a pris en sa protection Israël son serviteur;
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 Et comme il en avait parlé à nos pères, il s'est souvenu de sa miséricorde envers Abraham et sa postérité pour toujours. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Et Marie demeura avec elle environ trois mois; puis elle s'en retourna en sa maison.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Or, le terme d'Élisabeth étant venu, elle enfanta un fils.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Et ses voisins et ses parents, ayant appris que le Seigneur avait fait éclater sa miséricorde en sa faveur, s'en réjouissaient avec elle.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Et étant venus le huitième jour pour circoncire le petit enfant, ils l'appelaient Zacharie, du nom de son père.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Mais sa mère prit la parole et dit: Non, mais il sera nommé Jean.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Ils lui dirent: Il n'y a personne dans ta parenté qui soit appelé de ce nom.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Alors ils demandèrent par signe à son père comment il voulait qu'il fût nommé.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Et Zacharie ayant demandé des tablettes, écrivit ces mots: Jean est son nom; et ils en furent tous surpris.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 A l'instant sa bouche s'ouvrit, sa langue fut déliée, et il parlait en bénissant Dieu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Et tous leurs voisins furent remplis de crainte, et toutes ces choses se divulguèrent par tout le pays des montagnes de Judée.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Et tous ceux qui les entendirent, les conservèrent dans leur cœur, et disaient: Que sera donc ce petit enfant? Et la main du Seigneur était avec lui.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Alors Zacharie son père fut rempli du Saint-Esprit, et il prophétisa, en disant:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Béni soit le Seigneur, le Dieu d'Israël, de ce qu'il a visité et racheté son peuple,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Et de ce qu'il nous a suscité un puissant Sauveur, dans la maison de David son serviteur;
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 Comme il en avait parlé par la bouche de ses saints prophètes, depuis longtemps; (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 De ce qu'il nous a sauvés de nos ennemis, et de la main de tous ceux qui nous haïssent,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Pour exercer sa miséricorde envers nos pères, et se souvenir de sa sainte alliance,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 Savoir du serment qu'il avait fait à Abraham notre père,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 De nous accorder que, étant délivrés de la main de nos ennemis, nous le servirions sans crainte,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 Dans la sainteté et dans la justice, en sa présence, tous les jours de notre vie.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Et toi, petit enfant, tu seras appelé le prophète du Très-Haut; car tu marcheras devant la face du Seigneur, pour préparer ses voies,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Afin de donner la connaissance du salut à son peuple, dans la rémission de leurs péchés,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Par les entrailles de la miséricorde de notre Dieu, par lesquelles le soleil levant nous a visités d'en haut;
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Pour éclairer ceux qui sont assis dans les ténèbres et dans l'ombre de la mort, et pour conduire nos pas dans le chemin de la paix.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Et le petit enfant croissait et se fortifiait en esprit; et il demeura dans les déserts jusqu'au jour où il devait être manifesté à Israël.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luc 1 >