< Amos 3 >

1 Écoutez cette parole, que l'Éternel a prononcée contre vous, enfants d'Israël, contre toute la famille que j'ai fait monter du pays d'Égypte.
Ku ji wannan maganar da Ubangiji ya yi game da ku, ya ku jama’ar Isra’ila, a kan dukan iyalin da na fitar daga Masar.
2 Il a dit: Je n'ai connu que vous d'entre toutes les familles de la terre; c'est pourquoi je vous châtierai pour toutes vos iniquités.
“Ku ne kaɗai na zaɓa cikin dukan al’umman duniya; saboda haka zan hukunta ku saboda dukan zunubanku.”
3 Deux hommes marchent-ils ensemble, sans en être convenus?
Mutum biyu za su iya yin tafiya tare in ba su yarda su yi haka ba?
4 Le lion rugit-il dans la forêt, sans qu'il ait une proie? Le lionceau jette-t-il son cri de sa tanière, sans qu'il ait rien pris?
Zaki yakan yi ruri a jeji in bai sami kama nama ba? Zai yi gurnani a cikin kogonsa in bai kama kome ba?
5 L'oiseau tombe-t-il dans le filet qui est à terre, sans qu'il y ait un piège? Le filet se lève-t-il du sol, sans qu'il y ait rien de pris?
Tsuntsu yakan fāɗa a tarko a ƙasa inda ba a sa tarko ba, ko tarko yakan zargu daga ƙasa in ba abin da ya taɓa shi?
6 Si la trompette sonne dans une ville, le peuple ne sera-t-il pas alarmé? Et s'il arrive un malheur dans une ville, n'est-ce pas l'Éternel qui l'a fait?
Idan aka busa ƙaho a ciki birni mutane ba sa yin rawar jiki? Sa’ad da bala’i ya auko wa birni, ba Ubangiji ne ya sa a kawo shi ba?
7 Car le Seigneur, l'Éternel, ne fait rien, qu'il n'ait révélé son secret à ses serviteurs les prophètes.
Ba shakka, Ubangiji Mai Iko Duka ba ya yin wani abu ba tare da ya sanar wa bayinsa annabawa ba.
8 Le lion rugit: qui ne craindra? Le Seigneur, l'Éternel, parle: qui ne prophétisera?
Zaki ya yi ruri, wa ba zai tsorata ba? Ubangiji Mai Iko Duka ya yi magana, wa ba zai yi annabci ba?
9 Faites entendre votre voix sur les palais d'Asdod et sur les palais du pays d'Égypte, et dites: Assemblez-vous sur les montagnes de Samarie, et voyez quels désordres au milieu d'elle et quelles oppressions dans son sein!
Ku yi shela ga kagarun Ashdod da kuma ga kagarun Masar. “Ku tara kanku a tuddan Samariya; ku ga rashin jituwar da take a cikinta, da kuma zaluncin da ake yi a cikin mutanenta.”
10 Ils ne savent pas faire ce qui est droit, dit l'Éternel, ils amassent la violence et la rapine dans leurs palais.
“Ba su ma san yadda za su yi abin da yake daidai ba,” in ji Ubangiji, “sun ɓoye ganima da abubuwan da suka washe a cikin kagarunsu.”
11 C'est pourquoi, ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: L'ennemi vient, il entoure le pays; il abattra ta force et tes palais seront pillés.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Abokin gāba zai ƙwace ƙasar, zai saukar da mafakarku, zai washe kagarunku.”
12 Ainsi a dit l'Éternel: Comme un berger sauve de la gueule du lion deux jambes ou un bout d'oreille; ainsi seront sauvés les enfants d'Israël qui sont assis dans Samarie, à l'angle d'une couche et sur le damas d'un lit.
Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci daga bakin zaki ƙasusuwa ƙafafu biyu kawai ko kunne ɗaya, haka za a ceci Isra’ilawa, masu zama a Samariya da kan gado kawai da kuma a ɗan ƙyalle a kan dogayen kujerunsu.”
13 Écoutez et soyez mes témoins contre la maison de Jacob, dit le Seigneur, l'Éternel, le Dieu des armées:
“Ku ji wannan ku kuma yi wa gidan Yaƙub gargaɗi,” in ji Ubangiji, Ubangiji Allah Maɗaukaki.
14 Qu'au jour où je punirai Israël pour ses crimes, j'exercerai aussi la punition sur les autels de Béthel; les cornes de l'autel seront brisées et tomberont à terre.
“A ranar da zan hukunta Isra’ila saboda zunubanta, zan hallaka bagadan Betel; za a yayyanka ƙahonin bagadan za su fāɗa ƙasa
15 Et j'abattrai la maison d'hiver avec la maison d'été, les maisons d'ivoire périront, et de nombreuses maisons prendront fin, dit l'Éternel.
Zan rushe gidan rani da na damina; gidajen da aka yi musu ado da hauren giwa za a rushe su haka ma duk za a rurrushe manyan gidaje,” in ji Ubangiji.

< Amos 3 >