< Luc 8 >

1 Ensuite Jésus alla de ville en ville et de village en village, prêchant et annonçant la bonne nouvelle du royaume de Dieu.
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 Il était accompagné des Douze et de quelques femmes qu'il avait guéries des mauvais esprits et de leurs maladies; c’était Marie, appelée Madeleine, de laquelle étaient sortis sept démons,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 Jeanne, femme de Chouza, intendant d'Hérode, Suzanne et plusieurs autres qui l'assistaient de leurs biens, lui et ses disciples.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Un jour que s'était amassée une foule nombreuse, grossie de ceux qui de ville en ville venaient vers lui, il leur dit en parabole:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 «Un semeur sortit pour faire ses semailles; et, comme il semait, une partie de la semence tomba le long du chemin; elle fut foulée aux pieds, et les oiseaux du ciel la mangèrent.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Une autre partie tomba sur le roc: elle poussa et sécha, parce qu'elle manquait d'humidité.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Une autre partie tomba au milieu des épines; et les épines poussant avec la semence, l’étouffèrent.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 Enfin une autre partie tomba dans la bonne terre, elle poussa et produisit du fruit au centuple.» Puis il ajouta à haute voix: «Que celui qui a des oreilles pour entendre, entende.»
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Ses disciples lui ayant demandé ce que signifiait cette parabole,
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 il répondit: «Pour vous, il vous a été donné de connaître les mystères du royaume de Dieu; mais pour les autres, ce n'est qu'en paraboles, afin qu’en regardant, ils ne voient point, et qu'en entendant, ils ne comprennent point.»
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Voici donc le sens de cette parabole: La semence, c'est la parole de Dieu.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 Ceux qui reçoivent la semence le long du chemin, sont ceux qui entendent la Parole; ensuite le diable vient, et il l'enlève de leur coeur, de peur qu'ils ne croient et ne soient sauvés.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Ceux qui reçoivent la semence sur le roc, sont ceux qui reçoivent la Parole avec joie, dès qu'ils l'entendent, mais qui, n'ayant pas de racines, ne croient que pour un temps, et font défection au moment de l'épreuve.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Quant à la partie qui est tombée parmi les épines, ce sont ceux qui ont entendu la Parole, et qui, en cheminant, la laissent étouffer par les soucis, par les richesses et par les plaisirs de la vie, et ne donnent que des fruits avortés.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Quant à la partie qui est tombée dans la bonne terre, ce sont ceux qui entendent la Parole avec un coeur honnête et bon, la conservent, et portent du fruit avec persévérance.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 «Il n'est personne, qui, après avoir allumé une lampe, la couvre d'un vase, ou la mette sous un lit; mais on la met sur un pied, afin que ceux qui entrent voient clair.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Car il n'y a rien de caché qui ne se découvre, ni rien de secret qui ne finisse par être connu, et ne vienne au grand jour.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Prenez donc garde à la manière dont vous écoutez; car on donnera à celui qui a, mais pour celui qui n'a pas, on lui ôtera même ce qu'il croit avoir.»
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Cependant la mère et les frères de Jésus étaient venus le trouver, et ne pouvaient arriver jusqu’à lui, à cause de la foule.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 On l'en informa en lui disant: «Ta mère et tes frères sont là dehors, qui désirent te voir.»
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 Il répondit: «Ma mère et mes frères sont ceux qui écoutent la parole de Dieu, et qui la mettent en pratique.»
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Un jour il entra dans une barque avec ses disciples, et leur dit: «Passons de l'autre côté du lac; » et ils partirent.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 Pendant qu'ils naviguaient, Jésus s'endormit, et un ouragan ayant fondu sur le lac, la barque se remplissait d'eau; et ils étaient en péril.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Les disciples s'approchèrent de Jésus et le réveillèrent en disant: «Maître, maître, nous périssons.» Jésus se leva, tança lèvent et les flots: ils s'apaisèrent, et le calme se fit.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 Puis il dit à ses disciples: «où est votre foi?» Pour eux, saisis de frayeur et d'étonnement, ils se disaient les uns aux autres: «Quel est donc cet homme, qu'il commande aux vents et à l'eau, et qu'ils lui obéissent?»
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Puis ils abordèrent au pays des Gadaréniens, qui est vis-à-vis de la Galilée.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Quand Jésus fut descendu à terre, il rencontra un homme de la ville, qui depuis longtemps était possédé des démons: il ne portait point de vêtement, et demeurait non dans une maison, mais dans les sépulcres.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Dès qu'il vit Jésus, il poussa un cri, se jeta à ses pieds, et dit d'une voix forte: «Qu'y a-t-il entre toi et moi, Jésus, Fils du Dieu Très-Haut? Je t'en prie, ne me tourmente pas.»
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 Jésus, en effet, commandait à l'esprit impur de sortir de cet homme; car depuis longtemps l’esprit l'emportait avec lui: on avait beau le garder enchaîné et les fers aux pieds, il brisait ses liens et était entraîné par le démon dans les déserts.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Jésus lui demanda: «Quel est ton nom?» — «Légion, » répondit-il; en effet, plusieurs démons étaient entrés dans cet homme;
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 et il se mit à supplier Jésus de ne point commander à ces démons d'aller dans l'abîme. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Or, il y avait là un grand troupeau de pourceaux qui paissaient sur la montagne, et les démons le supplièrent de leur permettre d'aller dans ces pourceaux; et il le leur permit.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Étant donc sortis de cet homme, ils entrèrent dans les pourceaux, et le troupeau se rua du haut du précipice dans le lac, et se noya.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 A cette vue, les gardeurs s'enfuirent, et répandirent la nouvelle dans la ville et dans la campagne.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Les gens sortirent pour voir ce qui était arrivé; ils vinrent vers Jésus et trouvèrent l'homme de qui les démons étaient sortis, assis à ses pieds, vêtu et dans son bon sens; ce qui les remplit de frayeur.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Les témoins de ce fait leur rapportèrent aussi comment le démoniaque avait été guéri.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Toute la population de la contrée voisine des Gadaréniens le pria de s'éloigner de chez eux, parce qu'ils étaient en proie à une grande frayeur: Jésus étant entré dans la barque, s'en retourna.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 L'homme de qui les démons étaient sortis, lui demanda de rester avec lui, mais Jésus le renvoya en lui disant:
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 «Retourne dans ta maison, et raconte tout ce que Dieu a fait pour toi.» Il s'en alla, et publia par toute la ville tout ce que Jésus avait fait pour lui.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 A son retour, Jésus fut accueilli par la foule; car ils étaient tous à l'attendre.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 Alors il vint un homme nommé Jaïrus, chef de la synagogue, qui, se jetant aux pieds de Jésus, le supplia de venir dans sa maison,
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 parce qu'il avait une fille unique, d'environ douze ans, qui se mourait. Pendant que Jésus s'y acheminait, la foule le serrait à l'étouffer.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Et une femme qui était atteinte d'une hémorragie depuis douze ans, et qui avait dépensé tout son bien en médecins, sans qu'aucun d'eux eût pu la guérir,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 s'approcha par derrière, toucha la houppe de son manteau, et au même instant son hémorragie s'arrêta.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 Et Jésus dit: «Qui est-ce qui m'a touché?» Comme tous s'en défendaient, Pierre et ceux qui étaient avec lui, dirent: «Maître, la foule t'entoure et te presse, et tu demandes qui t'a touché!»
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 Mais Jésus répondit: «Quelqu'un m'a touché, car j'ai senti une vertu sortir de moi.»
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 La femme voyant qu'elle n'était pas restée inaperçue, vint toute tremblante se jeter aux pieds de Jésus, et déclara devant tout le monde, pour quelle cause elle l'avait touché, et comment elle avait été guérie à l'instant.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Jésus lui dit: «Ma fille, ta foi t'a guérie: va en paix.»
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 Il parlait encore, lorsqu'on vint de chez Jaïrus dire à ce chef de la synagogue: «Ta fille est morte, ne fatigue pas le Maître.»
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Mais Jésus, qui avait entendu cette parole, lui dit: «Ne crains point, crois seulement, et elle sera guérie.»
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 Lorsqu'il fut arrivé à la maison, il ne laissa entrer personne avec lui, si ce n'est Pierre, Jean, Jacques, avec le père et la mère de l'enfant.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Comme tous pleuraient et se lamentaient, Jésus leur dit: «Ne pleurez pas; elle n'est pas morte, mais elle dort.»
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 Et ils se moquèrent de lui, sachant qu'elle était morte.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 Mais lui, la saisissant par la main, dit en élevant la voix: «Enfant, lève-toi.»
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 La respiration lui revint, et elle se leva à l'instant; et Jésus commanda qu'on lui donnât à manger.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Les parents de la jeune fille furent dans le ravissement, et Jésus leur recommanda de ne dire à personne ce qui venait de se passer.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luc 8 >