< Luc 6 >

1 Le jour du second-premier sabbat, Jésus passant par des blés, ses disciples arrachaient des épis et les mangeaient, après les avoir froissés dans leurs mains.
A wata ranar Asabbaci, Yesu yana bi ta gonakin hatsi, sai almajiran suka fara kakkarya kan hatsi suna murjewa a hannuwansu suna ci.
2 Des pharisiens dirent: «Pourquoi faites-vous ce qui n'est pas permis le jour du sabbat?»
Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Me ya sa kuke yin abin da doka ta hana yi a ranar Asabbaci?”
3 Et Jésus prenant la parole, leur dit: «N'avez-vous pas lu ce que fit David, lorsqu'il eut faim, lui et ceux qui étaient avec lui:
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa ba?
4 comment il entra dans la maison de Dieu, prit les pains de proposition, en mangea, et en donna même à ceux qui l'accompagnaient, quoiqu'il ne soit permis qu'aux sacrificateurs d'en manger?»
Ya shiga gidan Allah, ya ɗauki keɓaɓɓen burodi, sa’an nan ya ci abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka. Ya kuma ba wa abokan tafiyarsa?”
5 Et il ajouta: «Le Fils de l'homme est maître même du sabbat.»
Sai Yesu ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum ne Ubangijin Asabbaci.”
6 Il lui arriva, un autre jour de sabbat, d'entrer dans la synagogue, et d'y enseigner. Il y avait là un homme dont la main droite était sèche.
A wata ranar Asabbaci kuma, Yesu ya shiga majami’a yana koyarwa. To, a nan kuwa akwai wani mutumin da hannun damansa ya shanye.
7 Les scribes et les pharisiens observaient Jésus, pour voir s'il faisait des guérisons le jour du sabbat, afin d'avoir sujet de l'accuser.
Farisiyawa da malaman dokoki suka zuba wa Yesu ido, su ga ko zai warkar a ranar Asabbaci, don su sami dalilin zarginsa.
8 Jésus pénétrant leurs pensées, dit à l'homme qui avait la main sèche: «Lève-toi, et tiens-toi là au milieu; » et lui, s'étant levé, se tint debout.
Amma Yesu ya san abin da suke tunani. Sai ya ce wa mutumin mai shanyayyen hannun, “Tashi ka tsaya a gaban kowa.” Sai ya tashi ya tsaya.
9 Jésus leur dit: «Je vous demande s'il est permis, le jour du sabbat, de faire bien ou de faire mal, de sauver la vie ou de l'ôter?»
Yesu ya ce musu, “Ina tambayarku, me ya kamata a yi bisa ga doka, a ranar Asabbaci, a aikata alheri ko a aikata mugunta, a ceci rai, ko a hallaka shi?”
10 Puis, ayant promené ses regards sur eux tous, il dit à cet homme: «Étends la main.» Il le fit, et sa main fut guérie.
Sai ya kalle su duka, sa’an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙe, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.
11 Les scribes et les pharisiens furent remplis de fureur; et ils conféraient ensemble pour savoir ce qu'ils feraient à Jésus.
Amma Farisiyawa da malaman Doka suka fusata, suka fara tattauna da junansu a kan abin da za su yi wa Yesu.
12 En ce temps-là, Jésus se rendit à la montagne pour prier Dieu, et il passa toute la nuit en prière.
Wata rana, a cikin kwanakin nan, Yesu ya je wani dutse domin yă yi addu’a, ya kuma kwana yana addu’a ga Allah.
13 Quand il fit jour, il appela ses disciples, et en choisit douze, auxquels il donna le nom d'Apôtres,
Da gari ya waye, sai ya kira almajiransa zuwa wurinsa, ya zaɓi guda goma sha biyu daga cikinsu, waɗanda ya kira su, Manzanni.
14 savoir, Simon, qu'il appela Pierre, et André son frère, Jacques, Jean, Philippe, Barthélemi,
Siman (wanda ya kira Bitrus), ɗan’uwansa Andarawus, Yaƙub, Yohanna, Filibus, Bartolomeyu,
15 Matthieu, Thomas, Jacques fils d'Alphée, Simon appelé le zélateur,
Mattiyu, Toma, Yaƙub ɗan Alfayus, Siman wanda ake kira Zilot,
16 Jude fils de Jacques, et Judas Iscariot, qui fut un traître.
Yahuda ɗan Yaƙub, da kuma Yahuda Iskariyot, wanda ya bashe Yesu.
17 Il descendit avec eux et s'arrêta sur un plateau, où se trouvaient une foule de ses disciples, et une multitude de gens qui étaient venus de toute là Judée, de Jérusalem et du littoral de Tyr et de Sidon, pour l'entendre et pour être guéris de leurs maladies.
Sai ya sauko tare da su, ya tsaya a wani fili. A can, akwai taro mai yawa na almajiransa, da kuma mutane masu yawan gaske daga ko’ina a Yahudiya, Urushalima da kuma Taya da Sidon da suke bakin teku,
18 Ceux qui étaient tourmentés par des esprits impurs étaient guéris;
waɗanda suka zo domin su ji shi, a kuma warkar da cututtukansu. Waɗanda suke fama da mugayen ruhohi kuwa aka warkar da su.
19 et toute la foule cherchait à le toucher, parce qu'il sortait de sa personne une vertu qui les guérissait tous.
Kuma dukan mutane suka yi ƙoƙari su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.
20 Alors, levant les yeux sur ses disciples, il dit: «Vous êtes bienheureux, vous qui êtes pauvres, parce que le royaume de Dieu est à vous.
Da ya dubi almajiransa, sai ya ce, “Masu albarka ne ku da kuke matalauta, gama mulkin Allah naku ne.
21 Vous êtes bienheureux, vous qui avez faim maintenant, parce que vous serez rassasiés. Vous êtes bienheureux, vous qui pleurez maintenant, parce que vous rirez.
Masu albarka ne ku da kuke jin yunwa yanzu, gama za ku ƙoshi. Masu albarka ne ku da kuke kuka yanzu, gama za ku yi dariya.
22 Bienheureux serez-vous, quand on vous haïra, quand on vous chassera, qu'on vous insultera et qu'on rejettera votre nom comme un nom infâme, à cause du Fils de l'homme.
Masu albarka ne sa’ad da mutane suka ƙi ku, suka ware ku, suka zage ku, suna ce da ku mugaye, saboda Ɗan Mutum.
23 Réjouissez-vous en ce jour-là et bondissez de joie, car votre récompense est grande dans le ciel: c'est ainsi que leurs pères traitaient les prophètes.
“Ku yi farin ciki a wannan rana, ku kuma yi tsalle don murna, saboda ladarku yana da yawa a sama. Gama haka kakanninsu suka yi wa annabawa.
24 Mais, malheur à vous, riches, parce que vous avez déjà votre consolation!
“Amma kaitonku da kuke da arziki, gama kun riga kun sami ta’aziyyarku.
25 Malheur à vous, rassasiés, parce que vous aurez faim! Malheur à vous, qui riez maintenant, parce que vous serez dans l'affliction et que vous pleurerez!
Kaitonku da kuke ƙosassu yanzu, gama za ku zauna da yunwa. Kaitonku da kuke dariya yanzu, gama za ku yi makoki da kuka.
26 Malheur à vous, lorsque tous les hommes diront du bien de vous, car c'est ce que leurs pères faisaient à l'égard des faux prophètes!
Kaitonku sa’ad da dukan mutane suna magana mai kyau a kanku, gama haka kakanninsu suka yi da annabawan ƙarya.
27 Mais je vous dis, à vous qui m'écoutez, aimez vos ennemis; faites du bien à ceux qui vous haïssent;
“Amma ina faɗa muku, ku da kuke ji na, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku yi wa masu ƙinku alheri.
28 bénissez ceux qui vous maudissent; priez pour ceux qui vous maltraitent.
Ku albarkaci waɗanda suke la’anta ku, ku kuma yi wa waɗanda suke wulaƙanta ku addu’a.
29 Si quelqu'un te frappe sur une joue, présente-lui l'autre, et si quelqu'un t'enlève ton manteau, laisse-lui prendre aussi ta tunique.
In wani ya mare ka a wannan kumatu, juya masa ɗayan ma, in wani ya ƙwace maka babban riga, kada ma ka hana masa’yar cikin ma.
30 Donne à tout homme qui te demande, et ne réclame pas ton bien à celui qui te le prend.
Duk wanda ya roƙe ka abu, ka ba shi. In kuma wani ya yi maka ƙwace, kada ka nema yă mayar maka.
31 Comme vous voulez que les hommes fassent pour vous, faites de même pour eux.
Ka yi wa waɗansu abin da kai kake so su yi maka.
32 Si vous aimez ceux qui vous aiment, quel gré vous en doit-on savoir? Les pécheurs aussi aiment ceux qui les aiment.
“In kana ƙaunar masu ƙaunarka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna ƙaunar waɗanda suke ƙaunarsu.
33 Si vous faites du bien à ceux qui vous en font, quel gré vous en doit-on savoir? Les pécheurs aussi en font autant.
In kuma kana yin alheri ga masu yi maka ne kaɗai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma suna yin haka.
34 Si vous prêtez à ceux de qui vous espérez être remboursés, quel gré vous en doit-on savoir?» Des pécheurs aussi prêtent à des pécheurs, afin qu'on leur rende la pareille.
In kana ba da bashi ga mutanen da za su iya biyan ka ne kawai, ina ribar wannan? Ko masu zunubi ma, suna ba da bashi ga masu zunubi, da fata za a biya su tsab.
35 Mais aimez vos ennemis, faites du bien, et prêtez sans rien espérer: votre récompense sera grande; et vous serez fils du Très-Haut, car il est bon envers les ingrats et les méchants.
Amma, ku ƙaunaci abokan gābanku, ku kuma yi musu alheri, ku ba su bashi, ba da sa zuciya sai an biya ku ba. Ta yin haka ne kawai, za ku sami lada mai yawa, ku kuma zama’ya’yan Mafi Ɗaukaka, gama shi mai alheri ne ga marasa godiya da mugaye.
36 Soyez donc miséricordieux, comme votre Père est miséricordieux.
Ku zama masu jinƙai, kamar yadda Ubanku mai jinƙai ne.
37 Ne jugez point, et vous ne serez point jugés; ne condamnez point, et vous ne serez point condamnés; absolvez, et l'on vous absoudra;
“Kada ku ɗora wa wani, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yanke wa wani hukunci, ku ma ba za a yanke muku ba. Ku gafarta, ku ma za a gafarta muku.
38 donnez, et l’on vous donnera: on vous donnera dans votre robe une bonne mesure, serrée, secouée et débordante; car on se servira pour vous de la même mesure avec laquelle vous aurez mesuré.
Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har yă yi tozo, yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna da shi, da shi za a auna muku.”
39 Il ajouta cette comparaison: «Un aveugle peut-il conduire un aveugle? Ne tomberont-ils pas tous deux dans une fosse?»
Ya kuma faɗa musu wannan misali cewa, “Makaho yana iya jagoran makaho ne? Ba sai dukansu biyu su fāɗa a rami ba?
40 Le disciple n'est pas au-dessus de son maître: tout disciple sera traité comme son maître.
Ɗalibi bai fi malaminsa ba, sai dai kowane ɗalibi wanda ya sami cikakkiyar koyarwa, zai zama kamar malaminsa.
41 Pourquoi vois-tu la paille qui est dans l'oeil de ton frère, tandis que tu ne remarques pas la poutre qui est dans ton oeil?
“Don me kake duban ɗan tsinke da yake idon ɗan’uwanka, amma ba ka kula da gungumen da yake a naka ido ba?
42 Ou comment peux-tu dire à ton frère: «Frère, laisse-moi ôter la paille qui est dans ton oeil, » toi qui ne vois pas la poutre qui est dans le tien? Hypocrite, ôte premièrement la poutre de ton oeil, alors tu verras à ôter la paille qui est dans l'oeil de ton frère;
Yaya za ka ce wa ɗan’uwanka, ‘Ɗan’uwa, bari in cire maka ɗan tsinke da yake idonka,’ alhali kuwa, kai kanka ka kāsa ganin gungumen da yake a naka ido? Kai munafuki! Ka fara cire gungumen daga idonka, sa’an nan za ka iya gani sosai, ka kuma cire ɗan tsinken da yake a idon ɗan’uwanka.”
43 car il n'y a pas de bon arbre qui produise de mauvais fruits, comme il n'y a pas de mauvais arbre qui produise de bons fruits:
“Ba itace mai kyau da yake ba da munanan’ya’ya. Mummunan itace kuma ba ya ba da’ya’ya masu kyau.
44 chaque arbre se reconnaît à son fruit. On ne cueille pas des figues sur des épines et l'on ne vendange pas le raisin sur la ronce.
Kowane itace da irin’ya’yansa ne ake saninsa. Mutane ba sa tsinke’ya’yan ɓaure daga ƙaya, ko kuwa’ya’yan inabi daga sarƙaƙƙiya.
45 L'homme de bien tire le bien du bon trésor de son coeur, et le méchant tire le mal de son mauvais trésor; car de l'abondance du coeur la bouche parle.
Mutumin nagari yakan nuna abubuwa nagari daga cikin nagarta da yake a ɓoye a zuciyarsa, mugun mutum kuwa yakan nuna mugayen abubuwa daga muguntar da take a ɓoye a zuciyarsa. Gama baki yakan faɗa abin da ya cika zuciya ne.”
46 Pourquoi m'appelez-vous: «Seigneur, Seigneur, » et ne faites-vous pas ce que je dis?
“Don me kuke ce da ni, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ amma ba kwa yin abin da na faɗa?
47 Je vous montrerai à qui ressemble tout homme qui vient à moi, qui écoute mes paroles et les met en pratique:
Zan nuna muku kwatancin mutumin da yakan zo wurina, yă ji kalmomina, yă kuma aikata.
48 il est semblable à un homme qui bâtit une maison, et qui, ayant creusé profondément, en a posé les fondements sur le roc: une inondation étant survenue, le fleuve est venu donner contre cette maison, et n'a pu l'ébranler, parce qu'elle était bien bâtie.
Yana kama da mutumin da ya gina gida, wanda ya haƙa ƙasa da zurfi, sa’an nan ya kafa tushen ginin a kan dutse. Da ambaliyar ruwa ta taso, ƙarfin ruwa kuwa ya buga gidan, wannan bai jijjiga shi ba, domin an yi masa tushen gini na ainihi.
49 Mais celui qui écoute et ne pratique pas, est semblable à un homme qui a bâti une maison sur la terre, sans creuser de fondements: le fleuve est venu donner contre cette maison, et aussitôt elle s'est écroulée; et la ruine de cette maison a été grande.
Amma wanda yakan ji kalmomina, ba ya kuma aikata su, yana kama da mutumin da ya gina gida a ƙasa, ba tare da ya kafa tushen gini ba. A sa’ad da ƙarfin ruwa ya buga gidan, sai gidan yă rushe, mummunar rushewa kuwa.”

< Luc 6 >