< Luc 1 >

1 Plusieurs ayant entrepris d'écrire l'histoire des événements qui se sont accomplis parmi nous,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 d'après ce que nous ont enseigné ceux qui en ont été les témoins oculaires dès le commencement, et qui sont devenus les ministres de la Parole,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 j'ai cru devoir aussi, après m'être soigneusement enquis de tous les faits, dès leur origine, te les raconter dans leur ordre, excellent Théophile,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 afin que tu reconnaisses la vérité des récits qui ont fait la matière de ton instruction.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Il y avait du temps d'Hérode, roi de Judée, un sacrificateur nommé Zacharie; il appartenait à la classe d'Abia, et sa femme, qui était une fille d'Aaron, se nommait Elisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Ils étaient tous deux justes devant Dieu, et observaient tous les commandements et ordonnances du Seigneur, de manière à être sans reproches.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Ils n'avaient point d'enfants, parce qu'Élisabeth était stérile; et ils étaient l'un et l'autre avancés en âge.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Quand vint le tour de sa classe, et qu'il dut officier devant Dieu,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 il fut désigné par le sort, selon les usages du sacerdoce, pour aller offrir les parfums dans le sanctuaire du Seigneur.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Pendant que tout le peuple était dehors en prières, à l'heure qu'on offre les parfums,
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 un ange du Seigneur lui apparut debout, à droite de l'autel des parfums.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Zacharie fut troublé à sa vue, et la frayeur s'empara de lui;
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 mais l'ange lui dit: «Ne crains point, Zacharie, car ta prière a été exaucée: Elisabeth, ta femme, te donnera un fils, et tu le nommeras Jean;
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 il sera pour toi un sujet de joie et d'allégresse, et beaucoup se réjouiront de sa naissance.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Car il sera grand devant le Seigneur; il ne boira ni vin, ni liqueur enivrante, et il sera rempli du Saint-Esprit dès le sein de sa mère;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 il convertira bien des fils d'Israël au Seigneur leur Dieu,
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 et lui-même marchera devant Dieu dans l'esprit et la vertu d'Élie, pour «ramener les coeurs des pères vers les enfants, » et les rebelles aux sentiments des justes, afin de préparer au Seigneur un peuple bien disposé.»
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Zacharie dit à l'ange: «A quoi reconnaîtrai-je la vérité de ce que tu m'annonces? car je suis vieux, et ma femme est déjà avancée en âge.»
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 L'ange lui répondit: «Je suis Gabriel, je me tiens devant Dieu; j'ai été envoyé pour te parler, et pour t'annoncer ces heureuses nouvelles.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Voici, tu seras muet, et tu ne pourras plus parler jusqu'au jour où se réalisera cette promesse, parce que tu n'as pas ajouté foi à mes paroles, qui s'accompliront en leur temps.»
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Cependant le peuple attendait Zacharie, et s'étonnait qu'il demeurât aussi longtemps dans le sanctuaire.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Quand Zacharie sortit, il ne pouvait leur parler; et ils comprirent qu'il avait eu une vision dans le sanctuaire, ce que lui-même confirmait par signes: et il resta muet.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Lorsque les jours de son office furent accomplis, il s'en retourna chez lui.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Quelque temps après, Elisabeth, sa femme, devint enceinte, et elle se tint cachée durant cinq mois, «parce que, disait-elle,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 c'est une grâce cachée que le Seigneur m'a faite, quand il a daigné ôter l'opprobre qui pesait sur moi aux yeux des hommes.»
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Au sixième mois, Dieu envoya l'ange Gabriel dans une ville de Galilée, appelée Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 vers une vierge fiancée à un homme de la famille de David, nommé Joseph. Cette vierge se nommait Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 L'ange lui dit en entrant: «Je te salue, toi qui es l'objet d'une grande grâce; le Seigneur est avec toi.»
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Cette parole la troubla; et elle se demandait ce que pouvait bien être cette salutation.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 L'ange lui dit: «Ne crains point, Marie, car tu as trouvé grâce devant Dieu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Tu concevras en ton sein, et tu enfanteras un fils; et tu lui donneras le nom de Jésus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Il sera grand; on l'appellera Fils du Très-Haut; le Seigneur Dieu lui donnera le trône de David, son père;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 il régnera éternellement sur la maison de Jacob, et son règne n'aura point de fin.» (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Mais Marie dit à l'ange: «Comment cela se fera-t-il, puisque je ne connais point d'homme?»
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 L'ange lui répondit: «Le Saint-Esprit viendra sur toi, et la puissance du Très-Haut te couvrira de son ombre; aussi l'être saint qui naîtra de toi, sera-t-il appelé Fils de Dieu.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Et voici, Elisabeth, ta parente, a, elle aussi, conçu un fils dans sa vieillesse, et celle qu'on appelait stérile est dans son sixième mois:
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 rien ne sera impossible à Dieu.»
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Marie lui dit: «Je suis la servante du Seigneur; qu'il me soit fait selon ta parole.» Et l'ange la quitta.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Dans ce même temps Marie partit, et s'en alla en hâte au pays des montagnes, dans une ville de Juda;
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 étant entrée dans la maison de Zacharie, elle salua Elisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Dès qu'Elisabeth eut entendu la salutation de Marie, son enfant tressaillit dans son sein, et elle fut remplie du Saint-Esprit.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Elle s'écria à haute voix: «Tu es bénie entre les femmes, et le fruit que tu portes est béni.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Et d'où me vient cet honneur, que la mère de mon Seigneur vienne me visiter?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Car, sitôt que la voix de ta salutation a frappé mon oreille, mon enfant a tressailli de joie dans mon sein.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Heureuse celle qui a cru à l'accomplissement de ce que le Seigneur lui a fait annoncer!»
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Et Marie dit: «Mon âme glorifie le Seigneur,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 et mon esprit est ravi de joie en Dieu, mon Sauveur,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 parce qu'il a jeté les yeux sur la bassesse de sa servante. «Car désormais toutes les générations me diront bienheureuse,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 parce que le Tout-Puissant a fait en moi de grandes choses: son nom est saint,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 et sa miséricorde détend d'âge en âge sur ceux qui le craignent.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Il a déployé la force de son bras; il a dissipé ceux qui s'enorgueillissaient dans les pensées de leurs coeurs;
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 il a renversé les puissants de leurs trônes, et il a élevé les petits;
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 il a comblé de biens les affamés, et il a renvoyé les riches les mains vides.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Il s'est intéressé à Israël son serviteur, et, comme il l'avait dit à nos pères, il s'est souvenu de sa miséricorde
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 envers Abraham et sa postérité, pour toujours.» (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Marie demeura avec Elisabeth, environ trois mois, puis elle s'en retourna dans sa maison.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Cependant Elisabeth, étant arrivée à son terme, mit au monde un fils.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Ses voisins et ses parents, ayant appris la grâce signalée que le Seigneur lui avait faite, l'en félicitèrent.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Le huitième jour, on vint circoncire l’enfant, et on lui donnait le nom de Zacharie, qui était le nom de son père,
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 lorsque sa mère prit la parole, et dit: «Non; il s'appellera Jean.»
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Ils lui dirent: «Il n'y a personne dans ta famille qui porte ce nom-là; »
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 et ils demandèrent par signes au père de l'enfant, comment il voulait qu'on le nommât.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Zacharie ayant demandé des tablettes, écrivit ces mots: «Son nom est Jean; » et ils en furent tous étonnés.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Au même instant, sa bouche s'ouvrit, sa langue se délia, il parlait, bénissant Dieu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 La crainte saisit tous les habitants des alentours, et, dans tout le pays des montagnes de la Judée, on parla de ces événements.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Tous ceux qui les apprirent, les serraient dans leur coeur en disant: «Que sera-donc cet enfant?» En effet, la main du Seigneur était avec lui.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Zacharie, son père, fut rempli du Saint-Esprit, et il prophétisa en ces termes:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 «Béni soit le Seigneur, le Dieu d'Israël, de ce qu'il a visité et racheté son peuple.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Il nous a suscité une Puissance libératrice dans la maison de David, son serviteur,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 selon qu'il en avait parlé par la bouche de ses saints prophètes des temps anciens, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 une Puissance qui nous délivrera de nos ennemis, et des mains de tous ceux qui nous haïssent.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Il a voulu faire miséricorde à nos pères, et il s'est souvenu de sa sainte alliance,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 selon la promesse qu'il avait faite par serment à Abraham, notre père,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 de nous donner, lorsque nous serions délivrés des mains de nos ennemis, de le servir sans crainte,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 en pratiquant sous son regard la sainteté et la justice tous les jours de notre vie.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 «Et toi, petit enfant, tu seras appelé prophète du Très-Haut; car tu marcheras devant la face du Seigneur, pour préparer ses voies,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 afin qu'il donne à son peuple la connaissance du salut par le pardon de ses péchés.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Car notre Dieu, dans ses tendres compassions, a fait lever d'en haut, sur nous, un soleil
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 qui doit éclairer ceux qui sont dans les ténèbres et dans l'ombre de la mort, afin de diriger nos pas dans le chemin de la paix.»
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Or, le petit enfant croissait, il se fortifiait en esprit; et il se tenait dans les déserts, jusqu'au jour où il se fit connaître à Israël.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luc 1 >