< Psaumes 92 >

1 Psaume de cantique, pour le jour du Sabbat. C'est une belle chose que de célébrer l'Eternel, et de psalmodier à ton Nom, ô Souverain!
Zabura ce. Waƙa ce. Domin ranar Asabbaci. Yana da kyau a yabi Ubangiji a kuma yi kiɗi ga sunanka, ya Mafi Ɗaukaka,
2 Afin d'annoncer chaque matin ta bonté et ta fidélité toutes les nuits.
don a yi shelar ƙaunarka da safe amincinka kuma da dare,
3 Sur l'instrument à dix cordes, et sur la musette, et par un Cantique [prémédité] sur la harpe.
da kiɗin molo mai tsirkiya goma da kuma ƙarar garaya.
4 Car, ô Eternel! tu m' as réjoui par tes œuvres; je me réjouirai des œuvres de tes mains.
Gama ka sa na yi murna ta wurin ayyukanka, ya Ubangiji; na rera don farin ciki saboda ayyukan hannuwanka.
5 Ô Eternel! que tes œuvres sont magnifiques! tes pensées sont merveilleusement profondes.
Ina misalin ayyukanka, ya Ubangiji, tunaninka da zurfi suke ƙwarai!
6 L'homme abruti n'y connaît rien, et le fou n'entend point ceci,
Mutum marar azanci ba zai sani ba, wawa ba zai gane ba,
7 [Savoir], que les méchants croissent comme l'herbe, et que tous les ouvriers d'iniquité fleurissent, pour être exterminés éternellement.
cewa ko da yake mugaye suna girma kamar ciyawa kuma dukan masu aikata mugunta suna haɓaka, za a hallaka su har abada.
8 Mais toi, ô Eternel! tu es haut élevé à toujours.
Amma kai, ya Ubangiji, za a ɗaukaka har abada.
9 Car voici tes ennemis, ô Eternel! car voici tes ennemis périront, [et] tous les ouvriers d'iniquité seront dissipés.
Gama tabbatacce abokan gābanka, ya Ubangiji, tabbatacce abokan gābanka za su hallaka; za a watsar da dukan masu aikata mugunta.
10 Mais tu élèveras ma corne comme celle d'une licorne, [et] mon onction sera d'une huile toute fraîche.
Ka ɗaukaka ƙahona kamar na ɓauna; an zubo mai masu kyau a kaina.
11 Et mon œil verra en ceux qui m'épient, et mes oreilles entendront touchant les malins, qui s'élèvent contre moi, [ce que je désire].
Idanuna sun ga fāɗuwar maƙiyana; kunnuwana sun ji kukan mugayen maƙiyana.
12 Le juste fleurira comme la palme, il croîtra comme le cèdre au Liban.
Adalai za su haɓaka kamar itacen dabino, za su yi girma kama al’ul na Lebanon;
13 Etant plantés dans la maison de l'Eternel, ils fleuriront dans les parvis de notre Dieu.
da aka daddasa a gidan Ubangiji, za su haɓaka a filayen gidan Allahnmu.
14 Encore porteront-ils des fruits dans la vieillesse toute blanche; ils seront en bon point, et demeureront verts;
Za su ci gaba da ba da’ya’ya a tsufansu, za su kasance ɗanye kuma kore shar,
15 Afin d'annoncer que l'Eternel [est] droit; c’est mon rocher, et il n'y a point d'injustice en lui.
suna shela cewa, “Ubangiji adali ne; shi ne Dutsena, kuma babu mugunta a cikinsa.”

< Psaumes 92 >