< Psaumes 85 >

1 Psaume des enfants de Coré, [donné] au maître chantre. Eternel, tu t'es apaisé envers ta terre, tu as ramené et mis en repos les prisonniers de Jacob.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Na’ya’yan Kora maza. Zabura ce. Ka nuna wa ƙasarka alheri, ya Ubangiji; ka mai da nasarorin Yaƙub.
2 Tu as pardonné l'iniquité de ton peuple, [et] tu as couvert tous leurs péchés; (Sélah)
Ka gafarta laifin mutanenka ka kuma shafe dukan zunubansu. (Sela)
3 Tu as retiré toute ta colère, tu es revenu de l'ardeur de ton indignation.
Ka kau da dukan fushinka ka kuma juye daga hasalar fushinka.
4 Ô Dieu de notre délivrance, rétablis-nous, et fais cesser la colère que tu as contre nous.
Ka sāke mai da mu, ya Allah Mai Cetonmu, ka kau da rashin jin daɗinka daga gare mu.
5 Seras-tu courroucé à toujours contre nous? feras-tu durer ta colère d'âge en âge?
Za ka ci gaba da fushi da mu har abada ne? Za ka ja fushinka cikin dukan tsararraki?
6 Ne reviendras-tu pas à nous rendre la vie, afin que ton peuple se réjouisse en toi?
Ba za ka sāke raya mu ba, don mutanenka su yi farin ciki a cikinka?
7 Eternel, fais-nous voir ta miséricorde, et accorde-nous ta délivrance.
Ka nuna mana ƙaunarka marar ƙarewa, ya Ubangiji, ka kuma ba mu cetonka.
8 J'écouterai ce que dira le [Dieu] Fort, l'Eternel; car il parlera de paix à son peuple et à ses bien-aimés, mais que [jamais] ils ne retournent à leur folie.
Zan saurari abin da Allah Ubangiji zai faɗa; ya yi alkawarin salama ga mutanensa, tsarkakansa, amma kada su koma ga wauta.
9 Certainement sa délivrance est proche de ceux qui le craignent, afin que la gloire habite en notre pays.
Tabbatacce cetonsa yana kusa da waɗanda suke tsoronsa, don ɗaukakarsa ta zauna a cikin ƙasarmu.
10 La bonté et la vérité se sont rencontrées; la justice et la paix se sont entre-baisées.
Ƙauna da aminci za su sadu; adalci da salama za su yi wa juna sumba.
11 La vérité germera de la terre, et la justice regardera des cieux.
Aminci zai ɓulɓulo daga ƙasa, adalci kuma yă duba daga sama.
12 L'Eternel aussi donnera le bien, tellement que notre terre rendra son fruit.
Ubangiji tabbatacce zai bayar da abin da yake da kyau, ƙasarmu kuwa za tă ba da amfaninta.
13 La justice marchera devant lui, et il la mettra partout où il passera.
Adalci na tafiya a gabansa yana shirya hanya domin ƙafafunsa.

< Psaumes 85 >