< Psaumes 61 >

1 Psaume de David, [donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Néguinoth. Ô Dieu écoute mon cri, sois attentif à ma requête.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da kayan kiɗi masu tsirkiya. Ta Dawuda. Ka ji kukata, ya Allah; ka saurari addu’ata.
2 Je crierai à toi du bout de la terre, lorsque mon cœur se pâme; conduis-moi sur cette roche, qui est trop haute pour moi.
Daga iyakar duniya na yi kira gare ka, na yi kira yayinda zuciyata ta karai; ka bishe ni zuwa dutsen da ya fi ni tsayi.
3 Car tu m'as été pour retraite, et pour une forte tour au-devant de l'ennemi.
Gama kai ne mafakata, hasumiya mai ƙarfi gāba da maƙiyi.
4 Je séjournerai dans ton Tabernacle durant un long temps; je me retirerai sous l'ombre de tes ailes; (Sélah)
Ina marmari in zauna a tentinka har abada in sami mafaka a cikin inuwar fikafikanka. (Sela)
5 Car tu as, ô Dieu! exaucé mes vœux, [et tu m'as] donné l'héritage de ceux qui craignent ton Nom.
Gama ka ji alkawarina, ya Allah; ka ba ni gādo na waɗanda suke tsoron sunanka.
6 Tu ajouteras des jours aux jours du Roi; [et] ses années seront comme plusieurs âges.
Ka ƙara kwanakin ran sarki, shekarunsa su kasance a zamanai masu yawa.
7 Il demeurera [à] toujours en la présence de Dieu; que la gratuité et la vérité le gardent!
Bari yă yi mulki a gaban Allah har abada; ka sa ƙaunarka da amincinka su tsare shi.
8 Ainsi je psalmodierai ton Nom à perpétuité, en [te] rendant mes vœux chaque jour.
Sa’an nan zan riƙa rera yabo ga sunanka in kuma cika alkawarina kowace rana.

< Psaumes 61 >