< Psaumes 58 >

1 Mictam de David, [donné] au maître chantre, [pour le chanter] sur Al-tasheth. En vérité, vous gens de l'assemblée, prononcez-vous ce qui est juste? Vous fils des hommes, jugez-vous avec droiture.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Kada Ka Hallaka.” Ta Dawuda. Wani miktam. Ku masu mulki tabbatacce kuna magana daidai? Kuna yin shari’a daidai a cikin mutane?
2 Au contraire, vous tramez des injustices dans votre cœur; vous balancez la violence de vos mains en la terre.
Sam, a zuciyarku kuna ƙirƙiro rashin adalci, da hannuwanku kuma kuna tā da hargitsi a duniya.
3 Les méchants se sont égarés dès la matrice, ils ont erré dès le ventre [de leur mère], en parlant faussement.
Kai, tun haihuwa mugaye sukan kauce; daga cikin ciki, su lalatattu ne maƙaryata.
4 Ils ont un venin semblable au venin du serpent, [et] ils sont comme l'aspic sourd, qui bouche son oreille;
Dafinsu ya yi kamar dafin maciji, kamar na gamsheƙan da ya toshe kunnuwansa,
5 Qui n'écoute point la voix des enchanteurs, [la voix] du charmeur fort expert en charmes.
da ba ya jin muryar gardi, kome dabarar gwanin mai waƙar zai zama.
6 Ô Dieu, brise-leur les dents dans leur bouche! Eternel, romps les dents mâchelières des lionceaux.
Ka kakkarya haƙoran a bakunansu, ya Allah; ka yayyage fiƙoƙin zakoki, ya Ubangiji!
7 Qu'ils s'écoulent comme de l'eau, et qu'ils se fondent! que [chacun d'eux] bande [son arc, mais] que ses flèches soient comme si elles étaient rompues!
Bari su ɓace kamar ruwa mai wucewa; sa’ad da suka ja bakansu, bari kibiyoyinsu su murtsuke.
8 Qu'il s'en aille comme un limaçon qui se fond! qu'ils ne voient point le soleil non plus que l'avorton d'une femme!
Kamar katantanwun da suke narkewa yayinda suke tafiya, kamar jinjirin da aka haifa matacce, kada su ga hasken rana.
9 Avant que vos chaudières aient senti le feu des épines, l'ardeur de la colère, semblable à un tourbillon, enlèvera [chacun d'eux] comme de la chair crue.
Kafin tukwanenka su ji zafin ƙayayyuwa, ko su kore ne ko busasshe, za a shafe mugaye.
10 Le juste se réjouira quand il aura vu la vengeance; il lavera ses pieds au sang du méchant.
Masu adalci za su yi murna sa’ad da aka rama musu, sa’ad da suka wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye.
11 Et chacun dira: quoi qu'il en soit, il y a une récompense pour le juste; quoi qu'il en soit, il y a un Dieu qui juge en la terre.
Sa’an nan mutane za su ce, “Tabbatacce har yanzu ana sāka wa adalai; tabbatacce akwai Allahn da yake shari’anta duniya.”

< Psaumes 58 >