< Nombres 31 >

1 L'Eternel parla aussi à Moïse, en disant:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Fais la vengeance des enfants d'Israël sur les Madianites, puis tu seras recueilli vers tes peuples.
“Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
3 Moïse donc parla au peuple, en disant: Que quelques-uns d'entre vous s'équipent pour aller à la guerre, et qu'ils aillent contre Madian, pour exécuter la vengeance de l'Eternel sur Madian.
Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
4 Vous enverrez à la guerre mille [hommes] de chaque Tribu, de toutes les tribus d'Israël.
Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
5 On donna donc d'entre les milliers d'Israël mille hommes de chaque Tribu, qui furent douze mille hommes équipés pour la guerre.
Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
6 Et Moïse les envoya à la guerre, [savoir] mille de chaque Tribu, et avec eux Phinées, fils d'Eiéazar le Sacrificateur, qui avait les vaisseaux du Sanctuaire, et les trompettes de retentissement en sa main.
Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
7 Ils marchèrent donc en guerre contre Madian, comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse, et ils en tuèrent tous les mâles.
Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
8 Ils tuèrent aussi les Rois de Madian, outre les autres qui y furent tués, [savoir] Evi, Rékem, Tsur, Hur, et Rébah, cinq Rois de Madian; ils firent aussi passer au fil de l'épée Balaam fils de Béhor.
A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
9 Et les enfants d'Israël emmenèrent prisonniers les femmes de Madian, avec leurs petits enfants, et pillèrent tout leur gros et menu bétail, et tout ce qui était en leur puissance.
Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
10 Ils brûlèrent au feu toutes leurs villes, leurs demeures, et tous leurs châteaux;
Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
11 Et ils prirent tout le butin et tout le pillage, tant des hommes que du bétail.
Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
12 Puis ils amenèrent les prisonniers, le pillage, et le butin, à Moïse et à Eléazar le Sacrificateur, et à l'assemblée des enfants d'Israël, au camp dans les campagnes de Moab, qui sont près du Jourdain de Jéricho.
suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
13 Alors Moïse et Eléazar le Sacrificateur, et tous les principaux de l'assemblée sortirent au devant d'eux hors du camp.
Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
14 Et Moïse se mit en grande colère contre les Capitaines de l'armée, les chefs des milliers, et les chefs des centaines, qui retournaient de cet exploit de guerre.
Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
15 Et Moïse leur dit: N'avez-vous pas gardé en vie toutes les femmes?
Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
16 Voici ce sont elles qui à la parole de Balaam, ont donné [occasion] aux enfants d'Israël de pécher contre l'Eternel au fait de Péhor [ce qui attira] la plaie sur l'assemblée de l'Eternel.
Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
17 Or maintenant tuez tous les mâles d'entre les petits enfants, et tuez toute femme qui aura eu compagnie d'homme.
Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
18 Mais vous garderez en vie toutes les jeunes filles qui n'ont point eu compagnie d'homme.
amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
19 Au reste, demeurez sept jours hors du camp. Quiconque tuera quelqu'un, et quiconque touchera quelqu'un qui aura été tué, se purifiera le troisième et le septième jour, tant vous que vos prisonniers.
“Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
20 Vous purifierez aussi tous vos vêtements, et tout ce qui sera fait de peau, et tous ouvrages de poil de chèvre, et toute vaisselle de bois.
Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
21 Et Eléazar le Sacrificateur dit aux hommes de guerre qui étaient allés à la bataille: Voici l'ordonnance et la Loi que l'Eternel a commandée à Moïse.
Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
22 En général l'or, l'argent, l'airain, le fer, l'étain, le plomb;
Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
23 Tout ce qui peut passer par le feu, vous le ferez passer par le feu, et il sera net; seulement on le purifiera avec l'eau d'aspersion; mais vous ferez passer par l'eau toutes les choses qui ne passent point par le feu.
da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
24 Vous laverez aussi vos vêtements le septième-jour, et vous serez nets, puis vous entrerez au camp.
A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
25 Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
26 Fais le compte du butin, et de tout ce qu'on a emmené, tant des personnes que des bêtes, toi et Eléazar le Sacrificateur, et les chefs des pères de l'assemblée.
“Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
27 Et partage par moitié le butin entre les combattants qui sont allés à la guerre, et toute l'assemblée.
Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
28 Tu lèveras aussi pour l'Eternel un tribut des gens de guerre qui sont allés à la bataille, [savoir] de cinq cents un, tant des personnes que des bœufs, des ânes et des brebis.
Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
29 On le prendra de leur moitié, et tu le donneras à Eléazar le Sacrificateur, en offrande élevée à l'Eternel.
Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
30 Et de l'[autre] moitié qui appartient aux enfants d'Israël, tu en prendras à part de cinquante un, tant des personnes que des bœufs, des ânes, des brebis et de tous [autres] animaux, et tu le donneras aux Lévites qui ont la charge de garder le pavillon de l'Eternel.
Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
31 Et Moïse et Eléazar le Sacrificateur firent comme l'Eternel l'avait commandé à Moïse.
Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
32 Or le butin, qui était resté du pillage que le peuple qui était allé à la guerre, avait fait, était de six cent soixante et quinze mille brebis;
Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
33 De soixante et douze mille bœufs;
shanu 72,000
34 De soixante et un mille ânes.
da jakuna 61,000.
35 Et quant aux femmes qui n'avaient point eu compagnie d'homme, [elles étaient] en tout trente-deux mille âmes.
Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
36 Et la moitié du butin, [savoir] la part de ceux qui étaient allés à la guerre, montait à trois cent trente-sept mille cinq cents brebis.
Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
37 Dont le tribut pour l'Eternel, quant aux brebis, fut de six cent soixante et quinze.
tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
38 Et à trente-six mille bœufs; dont le tribut pour l'Eternel, quant aux bœufs, fut de soixante et douze bœufs.
shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
39 Et à trente mille cinq cents ânes; dont le tribut pour l'Eternel, quant aux ânes, fut de soixante et un ânes.
jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
40 Et à seize mille personnes; dont le tribut pour l'Eternel fut de trente-deux personnes.
mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
41 Et Moïse donna à Eléazar le Sacrificateur le tribut de l'offrande élevée de l'Eternel, comme l'Eternel le lui avait commandé.
Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
42 Et de l'autre moitié qui appartenait aux enfants d'Israël, laquelle Moïse avait tirée des hommes qui étaient allés à la guerre.
Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
43 Or de cette moitié qui fut pour l'assemblée, et qui montait à trois cent trente-sept mille cinq cents brebis;
kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
44 A trente-six mille bœufs;
shanu 36,000,
45 A trente mille cinq cents ânes;
jakuna 30,500
46 Et à seize mille personnes;
da mutane 16,000.
47 De cette moitié, [dis-je], qui appartenait aux enfants d'Israël, Moïse prit à part de cinquante un, tant des personnes que des bêtes, et les donna aux Lévites qui avaient la charge de garder le pavillon de l'Eternel, comme l'Eternel le lui avait commandé.
Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
48 Et les capitaines qui avaient charge des milliers de l'armée, tant les chefs des milliers, que les chefs des centaines, s'approchèrent de Moïse,
Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
49 Et lui dirent: Tes serviteurs ont fait le compte des gens de guerre qui sont sous notre charge, et il ne s'en manque pas un seul.
suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
50 C'est pourquoi nous offrons l'offrande de l'Eternel, chacun ce qu'il s'est trouvé avoir, des joyaux d'or, des jarretières, des bracelets, des anneaux, des pendants d'oreilles, et des colliers, afin de faire propitiation pour nos personnes devant l'Eternel.
Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
51 Et Moïse et Eléazar le Sacrificateur reçurent d'eux l'or, [savoir] toute pièce d'ouvrage.
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
52 Et tout l'or de l'offrande élevée qui fut présenté à l'Eternel de la part des chefs de milliers et des chefs de centaines, [montait à] seize mille sept cent cinquante sicles.
Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
53 [Or] les gens de guerre retinrent chacun pour soi ce qu'ils avaient pillé.
Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
54 Moïse donc et Eléazar le Sacrificateur prirent des chefs de milliers et [des chefs] de centaines cet or-là, et l'apportèrent au Tabernacle d'assignation, [en] mémorial pour les enfants d'Israël, devant l'Eternel.
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.

< Nombres 31 >