< Nombres 27 >

1 Or les filles de Tsélophcad, fils de Hépher, fils de Galaad, fils de Makir, fils de Manassé, d'entre les familles de Manassé, fils de Joseph, s'approchèrent; et ce sont ici les noms de ces filles, Mahla, Noha, Hogla, Milca, et Tirtsa.
’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
2 Elles se présentèrent devant Moïse, devant Eléazar Sacrificateur, devant les principaux et devant toute l'assemblée, à l'entrée du Tabernacle d'assignation, [et] dirent:
Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
3 Notre père est mort au désert, qui toutefois n était point dans la troupe de ceux qui s'assemblèrent contre l'Eternel, [savoir] dans l'assemblée de Coré; mais il est mort dans son péché, et il n'a point eu de fils.
“Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
4 Pourquoi le nom de notre père serait-il retranché de sa famille, parce qu'il n'a point de fils? Donne-nous une possession parmi les frères de notre père.
Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
5 Et Moïse rapporta leur cause devant l'Eternel.
Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
6 Et l'Eternel parla à Moïse, en disant:
Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
7 Les filles de Tsélophcad parlent sagement. Tu ne manqueras pas de leur donner un héritage à posséder parmi les frères de leur père, et tu leur feras passer l'héritage de leur père.
“Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
8 Tu parleras aussi aux enfants d'Israël [et leur] diras: Quand quelqu'un mourra sans avoir des fils, vous ferez passer son héritage à sa fille.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
9 Que s'il n'a point de fille, vous donnerez son héritage à ses frères.
In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
10 Et s'il n'a point de frères, vous donnerez son héritage aux frères de son père.
In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
11 Que si son père n'a point de frère, vous donnerez son héritage à son parent, le plus proche de sa famille, et il le possédera; et ceci sera aux enfants d'Israël une ordonnance selon laquelle ils devront juger, comme l'Eternel l'a commandé à Moïse.
In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
12 L'Eternel dit aussi à Moïse: Monte sur cette montagne d'Abiram, et regarde le pays que j'ai donné aux enfants d'Israël.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
13 Tu le regarderas donc, et puis tu seras toi aussi recueilli vers tes peuples, comme Aaron ton frère y a été recueilli.
Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
14 Parce que vous avez été rebelles à mon commandement au désert de Tsin, dans la dispute de l'assemblée, [et] que vous ne m'avez point sanctifié au [sujet des] eaux devant eux; ce [sont] les eaux de la dispute de Kadès, au désert de Tsin.
gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
15 Et Moïse parla à l'Eternel, en disant:
Musa ya ce wa Ubangiji,
16 Que l'Eternel, le Dieu des esprits de toute chair, établisse sur l'assemblée quelque homme.
“Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
17 Qui sorte et entre devant eux, et qui les fasse sortir et entrer; et que l'assemblée de l'Eternel ne soit pas comme des brebis qui n'ont point de Pasteur.
yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
18 Alors l'Eternel dit à Moïse: Prends Josué, fils de Nun, qui est un homme en qui est l'Esprit, et tu poseras ta main sur lui.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
19 Tu le présenteras devant Eléazar le Sacrificateur, et devant toute l'assemblée; et tu l'instruiras en leur présence.
Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
20 Et tu lui feras part de ton autorité, afin que toute l'assemblée des enfants d'Israël l'écoute.
Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
21 Et il se présentera devant Eléazar le Sacrificateur, qui consultera pour lui par le jugement d'Urim devant l'Eternel; et à sa parole ils sortiront, et à sa parole ils entreront, lui, [et] les enfants d'Israël, avec lui, et toute l'assemblée.
Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
22 Moïse donc fit comme l'Eternel lui avait commandé, et prit Josué, et le présenta devant Eléazar le Sacrificateur, et devant toute l'assemblée.
Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
23 Puis il posa ses mains sur lui, et l'instruisit, comme l'Eternel l'avait commandé par le moyen de Moïse.
Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.

< Nombres 27 >