< Néhémie 6 >

1 Or il arriva que quand Samballat, Tobija, et Guésem Arabe, et le reste de nos ennemis eurent appris que j'avais rebâti la muraille, et qu'il n'y était demeuré aucune brèche, bien que jusqu'à ce temps-là, je n'eusse pas encore mis les battants aux portes;
Sa’ad da magana ta zo kunnen Sanballat, da Tobiya, da Geshem mutumin Arab da kuma sauran abokan gābanmu cewa na sāke gina katangar har babu sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake har zuwa lokacin ban sa ƙofofi a ƙyamare ba
2 Samballat et Guésem envoyèrent vers moi, pour me dire: Viens, et que nous nous trouvions ensemble aux villages qui sont à la campagne d'Ono. Or ils avaient comploté de me faire du mal.
Sanballat da Geshem suka aika mini wannan saƙo cewa, “Ka zo, mu sadu a wani ƙauye a filin Ono.” Amma makirci ne suke yi don su cuce ni;
3 Mais j'envoyai des messagers vers eux, pour leur dire: Je fais un grand ouvrage, et je ne saurais descendre. Pourquoi cesserait l'ouvrage, [comme cela arriverait] lorsque je l'aurais laissé, et que je serais descendu vers vous?
saboda haka sai na aika musu da wannan amsa, na ce, “Ina cikin babban aiki, ba zan kuwa iya gangarawa ba. Don me zan bar aikin yă tsaya don in gangara zuwa wurinku?”
4 Et ils me mandèrent la même chose quatre fois; et je leur répondis de même.
Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā.
5 Alors Samballat envoya vers moi son serviteur, pour me tenir le même discours une cinquième fois; et il avait en sa main une Lettre ouverte;
Sai sau na biya, Sanballat ya aiki mataimakinsa gare ni da irin saƙo guda, kuma a hannunsa akwai wasiƙar da ba a yimƙe ba
6 Dans laquelle il était écrit: On entend dire parmi les nations, et Gasmu le dit, que vous pensez, toi et les Juifs, à vous rebeller, et que c'est pour cela que tu rebâtis la muraille, et que tu t'en vas être le Roi, selon ce qu'on en dit;
wadda aka rubuta cewa, “An ba da labari cikin al’ummai, kuma Geshem ya ce gaskiya ne, cewa kai da Yahudawa kun shirya tawaye, saboda haka kuke sāke ginin katangar. Ban da haka ma, bisa ga waɗannan rahotanni kana shirin zaman sarkinsu
7 Et même que tu as ordonné des Prophètes pour te louer dans Jérusalem, et pour dire: Il est Roi en Judée. Or, maintenant, on fera entendre au Roi ces mêmes choses; viens donc maintenant afin que nous consultions ensemble.
har ma ka naɗa annabawa su yi wannan shela game da kai a Urushalima, su ce, ‘Akwai sarki a Yahuda!’ To, wannan rahoto zai koma wurin sarki; saboda haka ka zo, mu tattauna wannan batu.”
8 Et je renvoyai vers lui, pour lui dire: Ce que tu dis n'est point, mais tu l'inventes de toi-même.
Sai na aika masa wannan amsa, na ce, “Babu wani abu haka da yake faruwa; ka dai ƙaga wannan daga tunaninka ne.”
9 Car eux tous nous épouvantaient, en disant: Leurs mains quitteront le travail, de sorte qu'il ne se fera point. Maintenant donc, [ô Dieu!] renforce mes mains.
Suka dai yi ƙoƙari su tsoratar da mu, suna cewa, “Hannuwansu za su rasa ƙarfin yin aiki, ba kuwa za su ƙare aikin ba.” Amma na yi addu’a na ce, “Yanzu, ya Allah, ka ƙarfafa hannuwana.”
10 Outre cela, je vins en la maison de Sémahia, fils de Délaja, fils de Méhétabéel, lequel était retenu. Et il me dit: Assemblons-nous en la maison de Dieu, dans le Temple, et fermons les portes du Temple; car ils doivent venir pour te tuer, et ils viendront de nuit pour te tuer.
Wata rana na tafi gidan Shemahiya ɗan Delahiya, ɗan Mehetabel, wanda aka hana fita a gidansa. Ya ce mini, “Mu sadu gobe a gidan Allah, a cikin haikali, mu kuma kulle ƙofofin haikali, gama mutane suna zuwa su kashe ka, tabbatacce za su zo da dare su kashe ka.”
11 Mais je répondis: Un homme tel que moi s'enfuirait-il? Et qui sera l'homme tel que je suis, qui entre au Temple, pour sauver sa vie? Je n'y entrerai point.
Amma na ce, “Ya kamata mutum kamar ni yă gudu? Ko kuwa ya kamata wani kamar ni yă shiga cikin haikali don yă ceci ransa? Ba zan tafi ba!”
12 Et voilà, je connus bien que Dieu ne l'avait point envoyé; mais qu'il avait prononcé cette Prophétie contre moi, et que Samballat et Tobija lui donnaient pension,
Na gane cewa Allah bai aike shi ba, ya yi annabci a kaina domin Tobiya da Sanballat sun yi hayarsa ne.
13 Car il était leur pensionnaire pour m'épouvanter, et pour m'obliger à agir de la sorte, et à commettre cette faute, afin qu'ils eussent quelque mauvaise chose à me reprocher.
An yi hayarsa don yă sa in ji tsoro in yi zunubi ta yin haka, sa’an nan za su ba ni mugun suna, su wofinta ni.
14 Ô mon Dieu! souviens-toi de Tobija et de Samballat, selon leurs actions; et aussi de Nohadia prophétesse, et du reste des prophètes qui tâchaient de m'épouvanter.
Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat, saboda abin da suka yi; ka kuma tuna da annabiya Nowadiya da sauran annabawa waɗanda suke ƙoƙari su tsorata ni.
15 Néanmoins la muraille fut achevée le vingt-cinquième jour du mois d'Elul, en cinquante-deux jours.
Cikin kwana hamsin da biyu aka gama gina katangar, a ranar ashirin da biyar ga watan Elul.
16 Quand donc tous nos ennemis [l]'eurent appris, et que toutes les nations qui [étaient] autour de nous [l]'eurent vu, ils en furent tout consternés en eux-mêmes, et ils connurent que cet ouvrage avait été fait par le secours de notre Dieu.
Sa’ad da dukan abokan gābanmu suka ji haka, dukan al’umman da suke kewaye da mu suka ji tsoro, suka rasa ƙarfin halinsu, domin sun gane cewa wannan aiki an yi shi da taimakon Allahnmu ne.
17 Mais aussi en ces jours-là les principaux de Juda envoyaient Lettres sur Lettres qui allaient à Tobija; et celles de Tobija venaient à eux.
A waɗannan kwanaki, manyan garin Yahuda suka yi ta aika wasiƙu masu yawa zuwa ga Tobiya, shi kuma ya yi ta aika musu da amsoshi.
18 Car il y en avait plusieurs en Judée qui s'étaient liés à lui par serment, à cause qu'il était gendre de Séchania, fils d'Arah, et que Johanan, son fils avait pris la fille de Mésullam fils de Bérecia.
Gama mutane da yawa a cikin Yahuda sun rantse wa Tobiya za su goyi bayansa, domin ya auri’yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato, Yehohanan, ya auri’yar Meshullam, ɗan Berekiya.
19 Et même ils racontaient ses bienfaits en ma présence, et lui rapportaient mes discours; et Tobija envoyait des Lettres pour m'épouvanter.
Ban da haka ma, mutanen sun yi ta ba ni labarin ayyuka masu kyau da Tobiya ya yi, sa’an nan kuma suna faɗa masa duk abin da na faɗa. Tobiya kuwa ya aika wasiƙu don yă tsorata ni.

< Néhémie 6 >