< Michée 4 >

1 Mais il arrivera aux derniers jours, que la montagne de la maison de l'Eternel sera affermie au sommet des montagnes, et sera élevée par-dessus les coteaux; les peuples y aborderont.
A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
2 Et plusieurs nations iront, et diront: Venez, et montons à la montagne de l'Eternel, et à la maison du Dieu de Jacob; et il nous enseignera touchant ses voies, et nous marcherons dans ses sentiers; car la Loi sortira de Sion, et la parole de l'Eternel [sortira] de Jérusalem.
Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
3 Il exercera jugement parmi plusieurs peuples, et il censurera fortement les grandes nations jusqu'aux pays les plus éloignés; et de leurs épées elles forgeront des hoyaux; et de leurs hallebardes, des serpes; une nation ne lèvera plus l'épée contre l'autre, et elles ne s'adonneront plus à la guerre.
Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
4 Mais chacun s'assiéra sous sa vigne et sous son figuier, et il n'y aura personne qui les épouvante; car la bouche de l'Eternel des armées a parlé.
Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
5 Certainement tous les peuples marcheront chacun au nom de son dieu; mais nous marcherons au nom de l'Eternel notre Dieu à toujours et à perpétuité.
Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
6 En ce temps-là, dit l'Eternel, j'assemblerai la boiteuse, et je recueillerai celle qui avait été chassée, et celle que j'avais affligée.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
7 Et je mettrai la boiteuse, pour être un résidu, et celle qui était éloignée, pour être une nation robuste; l'Eternel régnera sur eux en la montagne de Sion dès cette heure-là à toujours.
Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
8 Et toi, Tour du troupeau, Hophel, la fille de Sion viendra jusqu'à toi; et la première domination viendra, le Royaume, [dis-je], viendra à la fille de Jérusalem.
Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
9 Pourquoi t'écries-tu maintenant si fort? N'y a-t-il point de Roi au milieu de toi? Ou ton conseiller est-il péri, que la douleur t'ait saisie comme de celle qui enfante?
Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
10 Sois en travail, et crie, fille de Sion, comme celle qui enfante; car tu sortiras bientôt de la ville, et tu demeureras aux champs, et viendras jusqu'à Babylone; [mais] là tu seras délivrée; là l'Eternel te rachètera des mains de tes ennemis.
Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
11 Et maintenant se sont assemblées contre toi plusieurs nations qui disent: Qu'elle soit profanée, et que notre œil voie en Sion [ce qu'il y voudrait voir].
Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
12 Mais ils ne connaissent point les pensées de l'Eternel, et n'entendent point son conseil; car il les a assemblées comme des gerbes dans l'aire.
Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
13 Lève-toi, et foule, fille de Sion, car je ferai que ta corne sera de fer, et je ferai que tes ongles seront d'airain; et tu menuiseras plusieurs peuples, et je dédierai comme un interdit leur gain à l'Eternel, et leurs biens au Seigneur de toute la terre.
“Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.

< Michée 4 >