< Luc 17 >

1 Or il dit à ses Disciples: il ne se peut faire qu'il n'arrive des scandales; mais malheur à celui par qui ils arrivent.
Sai Yesu ya ce wa almajiransa, 'Babu shakka akwai sanadodin tuntube da za su sa mu yin zunubi amma kaiton wanda shine sanadin su!
2 Il lui vaudrait mieux qu'on lui mît une pierre de meule autour de son cou, et qu'il fût jeté dans la mer, que de scandaliser un seul de ces petits.
Zai gwammaci a rataya masa dutsen nika a wuyansa, a jefar da shi a cikin teku fiye da wanda zai zama sanadiyar tuntube ga wadannan kananan.
3 Soyez attentifs sur vous-mêmes. Si donc ton Frère a péché contre toi, reprends-le; et s'il se repent, pardonne-lui.
Ku kula da kanku. Idan dan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa, in kuwa ya tuba ka yafe masa.
4 Et si sept fois le jour il a péché contre toi, et que sept fois le jour il retourne à toi, disant: je me repens; tu lui pardonneras.
Idan ya yi maka laifi sau bakwai a rana daya sa'annan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, 'Na tuba,' ya wajabta ka yafe masa!”
5 Alors les Apôtres dirent au Seigneur: augmente-nous la foi.
Sai Manzannin suka ce wa Ubangiji, 'Ka kara mana bangaskiya.'
6 Et le Seigneur dit: si vous aviez de la foi aussi gros qu'un grain de semence de moutarde, vous pourriez dire à ce mûrier: déracine-toi, et te plante dans la mer; et il vous obéirait.
Ubangiji kuwa ya ce, “In kuna da bangaskiya kamar kwayar mastad, za ku ce wa wannan durumin, 'Ka tuge, ka kuma dasu a cikin teku,' zai yi biyayya da ku.
7 Mais qui est celui d'entre vous qui ayant un serviteur labourant, ou paissant le bétail, et qui le voyant retourner des champs, lui dise incontinent: avance-toi, et mets-toi à table;
Amma wanene a cikinku, idan yana da bawa mai yin masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce masa, 'Maza zo ka zauna ka ci abinci'?
8 Et qui plutôt ne lui dise: apprête-moi à souper, ceins-toi, et me sers jusqu'à ce que j'aie mangé et bu; et après cela tu mangeras et tu boiras?
Ba zai ce masa, 'Ka shirya mani wani abu domin in ci ka kuma yi damara, ka yi mini hidima har in gama ci da sha. Bayan haka sai ka ci ka sha'?
9 Mais est-il pour cela obligé à ce serviteur de ce qu'il a fait ce qu'il lui avait commandé? Je ne le pense pas.
Ba zai yi wa bawan nan godiya ba domin ya yi biyayya da abubuwan da aka umarce shi ya yi, ko zai yi haka?
10 Vous aussi de même, quand vous aurez fait toutes les choses qui vous sont commandées, dites: nous sommes des serviteurs inutiles; parce que ce que nous avons fait, nous étions obligés de le faire.
Haka kuma, idan kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, 'Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibi ne kurum.'”
11 Et il arriva qu'en allant à Jérusalem, il passait par le milieu de la Samarie, et de la Galilée.
Wata rana yana tafiya zuwa Urushalima, sai ya bi iyakar kasar Samariya da Galili.
12 Et comme il entrait dans une bourgade, dix hommes lépreux le rencontrèrent, et ils s'arrêtèrent de loin;
Yayin da yana shiga wani kauye kenan, sai wadansu kutare maza guda goma suka tarye shi suna tsaye daga nesa da shi
13 Et élevant leur voix, ils lui dirent: Jésus, Maître, aie pitié de nous.
sai suka daga murya suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka yi mana jinkai.”
14 Et quand il les eut vus, il leur dit: allez, montrez-vous aux Sacrificateurs. Et il arriva qu'en s'en allant ils furent rendus nets.
Da ya gan su, ya ce masu, “Ku je ku nuna kanku a wurin firistoci.” Ya zama sa'adda suke tafiya, sai suka tsarkaka.
15 Et l'un d'eux voyant qu'il était guéri, s'en retourna, glorifiant Dieu à haute voix;
Daya daga cikinsu da ya ga an warkar da shi, ya koma, yana ta daukaka Allah da murya mai karfi.
16 Et il se jeta en terre sur sa face aux pieds de Jésus, lui rendant grâces. Or c'était un Samaritain.
Ya fadi a gaban Yesu, yana masa godiya. Shi kuwa Basamariye ne.
17 Alors Jésus prenant la parole, dit: les dix n'ont-ils pas été rendus nets? et les neuf où sont-ils?
Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina sauran taran?
18 Il n'y a eu que cet étranger qui soit retourné pour rendre gloire à Dieu.
Babu wani da ya dawo ya girmama Allah sai wannan bakon kadai?”
19 Alors il lui dit: lève-toi; va-t'en, ta foi t'a sauvé.
Sai ya ce masa, “Tashi, kayi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Or étant interrogé par les Pharisiens, quand viendrait le Règne de Dieu; il répondit, et leur dit: le Règne de Dieu ne viendra point avec apparence.
Da Farisawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai bayyana, Yesu ya amsa masu ya ce, “Mulkin Allah ba lura ake yi da shi ba.
21 Et on ne dira point: voici, il est ici; ou voilà, il est là; car voici, le Règne de Dieu est au-dedans de vous.
Ba kuwa za a ce, 'Gashi nan!' Ko kuwa, 'Ga shi can ba!' domin mulkin Allah yana tsaknaninku.”
22 Il dit aussi à ses Disciples: les jours viendront que vous désirerez de voir un des jours du Fils de l'homme, mais vous ne [le] verrez point.
Yesu ya ce wa almajiran, “Kwanaki na zuwa da za ku yi begen ganin rana daya cikin ranakun Dan Mutum, amma ba zaku gani ba.
23 Et l'on vous dira: voici, il est ici; ou voilà, il est là; [mais] n'y allez point, et ne les suivez point.
Za su ce maku, 'Duba can! 'Duba nan!' Amma kada ku je kuna dubawa, ko kuwa ku bi su.
24 Car comme l'éclair brille de l'un des côtés de dessous le ciel, et reluit jusques à l'autre qui est sous le ciel, tel sera aussi le Fils de l'homme en son jour.
Kamar yadda walkiya take haskakawa daga wannan bangaren sararin sama zuwa wancan bangaren, haka ma dan mutum zai zama a ranar bayyanuwarsa.
25 Mais il faut premièrement qu'il souffre beaucoup, et qu'il soit rejeté par cette nation.
Amma lalle sai ya sha wahaloli dabam dabam tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ki shi.
26 Et comme il arriva aux jours de Noé, il arrivera de même aux jours du Fils de l'homme.
Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Dan Mutum.
27 On mangeait et on buvait; on prenait et on donnait des femmes en mariage jusqu'au jour que Noé entra dans l'Arche; et le déluge vint qui les fit tous périr.
Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har zuwa ga ranar da Nuhu ya shiga jirgi - ruwan tufana kuma ya zo, ya hallaka su duka.
28 Il arriva aussi la même chose aux jours de Lot: on mangeait, on buvait, on achetait, on vendait, on plantait et on bâtissait;
Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine.
29 Mais au jour que Lot sortit de Sodome, il plut du feu et du soufre du ciel, qui les fit tous périr.
Amma a ranar da Lutu, ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da kibiritu daga sama, aka hallaka su duka.
30 Il en sera de même au jour que le Fils de l'homme sera manifesté.
Haka kuma zai zama a ranar bayyanuwar Dan Mutum.
31 En ce jour-là que celui qui sera sur la maison, et qui aura son ménage dans la maison, ne descende point pour l'emporter; et que celui qui sera aux champs, ne retourne point non plus à ce qui est demeuré en arrière.
A ranar nan fa, wanda yake kan soro kada ya sauka domin daukan kayansa daga cikin gida. Haka kuma wanda yake gona kada ya dawo.
32 Souvenez-vous de la femme de Lot.
Ku tuna fa da matar Lutu.
33 Quiconque cherchera à sauver sa vie, la perdra; et quiconque la perdra, la vivifiera.
Duk mai son ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai same shi.
34 Je vous dis, qu'en cette nuit-là deux seront dans un même lit: l'un sera pris, et l'autre laissé.
Ina gaya maku, a wannan dare za a sami mutum biyu a gado daya. Za a dauka daya, a kuma bar dayan.
35 Il y aura deux [femmes] qui moudront ensemble: l'une sera prise, et l'autre laissée.
Za a sami mata biyu suna nika tare. Za a dauka daya a bar daya.”
36 Deux seront aux champs: l'un sera pris, et l'autre laissé.
[“Za a ga mutum biyu a gona. Za a dauki daya a bar daya.”]
37 Et eux répondant lui dirent: où [sera-ce] Seigneur? et il leur dit: en quelque lieu que sera le corps [mort], là aussi s'assembleront les aigles.
Sai suka tambaye shi, “Ina, Ubangiji?” Sai ya ce masu, “Duk in da gangar jiki yake, a nan ungulai sukan taru.”

< Luc 17 >