< Luc 17 >

1 Or il dit à ses Disciples: il ne se peut faire qu'il n'arrive des scandales; mais malheur à celui par qui ils arrivent.
Yesu ya ce wa almajiransa, “Dole ne a sami abubuwan da suke sa mutane su yi zunubi, amma kaiton mutumin nan wanda suke zuwa ta wurinsa.
2 Il lui vaudrait mieux qu'on lui mît une pierre de meule autour de son cou, et qu'il fût jeté dans la mer, que de scandaliser un seul de ces petits.
Gwamma a ɗaura dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku, da ya sa ɗaya daga cikin ƙananan yaran nan ya yi zunubi.
3 Soyez attentifs sur vous-mêmes. Si donc ton Frère a péché contre toi, reprends-le; et s'il se repent, pardonne-lui.
Saboda haka, ku lura da kanku. “In ɗan’uwanka ya yi zunubi, ka kwaɓe shi. In ya tuba, ka gafarta masa.
4 Et si sept fois le jour il a péché contre toi, et que sept fois le jour il retourne à toi, disant: je me repens; tu lui pardonneras.
In ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, ya kuma dawo sau bakwai ɗin a wurinka, yana cewa, ‘Na tuba,’ sai ka gafarta masa.”
5 Alors les Apôtres dirent au Seigneur: augmente-nous la foi.
Sai manzannin suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya!”
6 Et le Seigneur dit: si vous aviez de la foi aussi gros qu'un grain de semence de moutarde, vous pourriez dire à ce mûrier: déracine-toi, et te plante dans la mer; et il vous obéirait.
Ya amsa musu ya ce, “In kuna da bangaskiya da take ƙanƙani kamar ƙwayar mustad, kuna iya ce wa wannan itacen durumi, ‘Ka tumɓuke daga nan, ka dasu a cikin teku.’ Zai kuwa yi muku biyayya.
7 Mais qui est celui d'entre vous qui ayant un serviteur labourant, ou paissant le bétail, et qui le voyant retourner des champs, lui dise incontinent: avance-toi, et mets-toi à table;
“In ɗaya a cikinku yana da bawa, wanda yake masa noma, ko kiwon tumaki, da dawowar bawan daga gonar, ai, ba zai ce masa, ‘Ka zo nan, ka zauna, ka ci abinci ba’?
8 Et qui plutôt ne lui dise: apprête-moi à souper, ceins-toi, et me sers jusqu'à ce que j'aie mangé et bu; et après cela tu mangeras et tu boiras?
Ashe, ba zai ce masa, ‘Ka shirya mini abincin yamma, ka shirya ka yi mini hidima domin in ci in sha, bayan haka kana iya ci, ka kuma sha ba’?
9 Mais est-il pour cela obligé à ce serviteur de ce qu'il a fait ce qu'il lui avait commandé? Je ne le pense pas.
Shin, zai gode wa bawan don yă yi aikin da aka ce ya yi ne?
10 Vous aussi de même, quand vous aurez fait toutes les choses qui vous sont commandées, dites: nous sommes des serviteurs inutiles; parce que ce que nous avons fait, nous étions obligés de le faire.
Haka ku ma, bayan kun yi duk abin da aka ce muku ku yi, ya kamata ku ce, ‘Mu bayi ne marasa cancanta, mun dai yi aikinmu ne kaɗai.’”
11 Et il arriva qu'en allant à Jérusalem, il passait par le milieu de la Samarie, et de la Galilée.
Yesu yana kan hanyarsa zuwa Urushalima, sai ya bi takan iyakar Samariya da Galili.
12 Et comme il entrait dans une bourgade, dix hommes lépreux le rencontrèrent, et ils s'arrêtèrent de loin;
Da zai shiga wani ƙauye, sai maza goma da suke da kuturta suka sadu da shi. Suka tsaya da nesa,
13 Et élevant leur voix, ils lui dirent: Jésus, Maître, aie pitié de nous.
suka yi kira da babbar murya, suka ce, “Yesu, Ubangiji, ka ji tausayinmu!”
14 Et quand il les eut vus, il leur dit: allez, montrez-vous aux Sacrificateurs. Et il arriva qu'en s'en allant ils furent rendus nets.
Da ya gan su sai ya ce, “Ku je ku nuna kanku ga firistoci.” Suna kan hanyar tafiya sai suka tsabtacce.
15 Et l'un d'eux voyant qu'il était guéri, s'en retourna, glorifiant Dieu à haute voix;
Da ɗayansu ya ga ya warke, sai ya koma, yana yabon Allah da babbar murya.
16 Et il se jeta en terre sur sa face aux pieds de Jésus, lui rendant grâces. Or c'était un Samaritain.
Ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya gode masa. Shi kuwa mutumin Samariya ne.
17 Alors Jésus prenant la parole, dit: les dix n'ont-ils pas été rendus nets? et les neuf où sont-ils?
Yesu ya yi tambaya ya ce, “Ba duka goma ne aka tsabtacce ba? Ina sauran taran?
18 Il n'y a eu que cet étranger qui soit retourné pour rendre gloire à Dieu.
Ba wanda ya dawo don yă yabi Allah, sai dai wannan baƙon?”
19 Alors il lui dit: lève-toi; va-t'en, ta foi t'a sauvé.
Sai ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.”
20 Or étant interrogé par les Pharisiens, quand viendrait le Règne de Dieu; il répondit, et leur dit: le Règne de Dieu ne viendra point avec apparence.
Wata rana, Farisiyawa suka tambaye shi lokacin da mulkin Allah zai zo, Yesu ya amsa ya ce, “Ai, mulkin Allah ba takan zo ta wurin yin kallon ku ba.
21 Et on ne dira point: voici, il est ici; ou voilà, il est là; car voici, le Règne de Dieu est au-dedans de vous.
Mutane kuma ba za su ce, ‘Ga shi nan,’ ko kuma, ‘Ga shi can’ ba, domin mulkin Allah yana cikinku ne.”
22 Il dit aussi à ses Disciples: les jours viendront que vous désirerez de voir un des jours du Fils de l'homme, mais vous ne [le] verrez point.
Sai ya ce wa almajiransa, “Lokaci yana zuwa da za ku yi marmarin ganin rana ɗaya cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba.
23 Et l'on vous dira: voici, il est ici; ou voilà, il est là; [mais] n'y allez point, et ne les suivez point.
Mutane za su ce muku, ‘Ga shi can!’ Ko kuma, ‘Ga shi nan!’ Kada ku yi hanzarin binsu.
24 Car comme l'éclair brille de l'un des côtés de dessous le ciel, et reluit jusques à l'autre qui est sous le ciel, tel sera aussi le Fils de l'homme en son jour.
Gama Ɗan Mutum, a cikin ranarsa, zai zama kamar walƙiya da take walƙawa, da take kuma haskaka sararin sama, daga wannan kusurwa zuwa wancan kusurwa.
25 Mais il faut premièrement qu'il souffre beaucoup, et qu'il soit rejeté par cette nation.
Amma da fari, dole yă sha wahaloli masu yawa, kuma mutanen zamanin nan su ƙi shi.
26 Et comme il arriva aux jours de Noé, il arrivera de même aux jours du Fils de l'homme.
“Daidai kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a zamanin Ɗan Mutum.
27 On mangeait et on buvait; on prenait et on donnait des femmes en mariage jusqu'au jour que Noé entra dans l'Arche; et le déluge vint qui les fit tous périr.
Mutane suna ci, suna sha, suna aurayya, ana kuma ba da su ga aure, har ranar da Nuhu ya shiga jirgin. Sa’an nan ambaliyar ruwan ya sauka, ya hallaka su duka.
28 Il arriva aussi la même chose aux jours de Lot: on mangeait, on buvait, on achetait, on vendait, on plantait et on bâtissait;
“Haka ma aka yi a zamanin Lot. Mutane suna ci, suna sha, suna saya, suna sayarwa, suna shuki, suna kuma gine-gine.
29 Mais au jour que Lot sortit de Sodome, il plut du feu et du soufre du ciel, qui les fit tous périr.
Amma a ranar da Lot ya bar Sodom, sai aka yi ruwan wuta da farar wuta daga sama, aka hallaka su duka.
30 Il en sera de même au jour que le Fils de l'homme sera manifesté.
“Daidai haka zai zama, a ranar da Ɗan Mutum zai bayyana.
31 En ce jour-là que celui qui sera sur la maison, et qui aura son ménage dans la maison, ne descende point pour l'emporter; et que celui qui sera aux champs, ne retourne point non plus à ce qui est demeuré en arrière.
A ranan nan, kada wanda yake kan rufin gidansa ya sauka don yă kwashe dukiyarsa da take cikin gidan. Haka ma duk wanda yake gona, kada yă koma don wani abu.
32 Souvenez-vous de la femme de Lot.
Ku tuna fa da matar Lot!
33 Quiconque cherchera à sauver sa vie, la perdra; et quiconque la perdra, la vivifiera.
Duk wanda yake so ya ceci ransa, zai rasa shi, amma duk wanda ya rasa ransa, zai cece shi.
34 Je vous dis, qu'en cette nuit-là deux seront dans un même lit: l'un sera pris, et l'autre laissé.
Ina gaya muku, a daren nan, mutane biyu za su kasance a gado ɗaya, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.
35 Il y aura deux [femmes] qui moudront ensemble: l'une sera prise, et l'autre laissée.
Mata biyu za su kasance suna niƙan hatsi tare, za a ɗauki ɗaya, a bar ɗayan.”
36 Deux seront aux champs: l'un sera pris, et l'autre laissé.
37 Et eux répondant lui dirent: où [sera-ce] Seigneur? et il leur dit: en quelque lieu que sera le corps [mort], là aussi s'assembleront les aigles.
Suka tambaya, suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “Ai, inda gawa take, nan ne ungulai za su taru.”

< Luc 17 >