< Luc 1 >

1 Parce que plusieurs se sont appliqués à mettre par ordre un récit des choses qui ont été pleinement certifiées entre nous;
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Comme nous les ont donné à connaître ceux qui les ont vues eux-mêmes dès le commencement, et qui ont été les Ministres de la parole.
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 Il m'a aussi semblé bon, après avoir examiné exactement toutes choses depuis le commencement jusques à la fin, très-excellent Théophile, de t'en écrire par ordre;
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Afin que tu connaisses la certitude des choses dont tu as été informé.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Au temps d'Hérode Roi de Judée, il y avait un certain Sacrificateur nommé Zacharie, du rang d'Abia; et sa femme [était] des filles d'Aaron, et son nom était Elisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Et ils étaient tous deux justes devant Dieu, marchant dans tous les commandements, et dans [toutes] les ordonnances du Seigneur, sans reproche.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Et ils n'avaient point d'enfants, à cause qu'Elisabeth était stérile; et qu'ils étaient fort avancés en âge.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Or il arriva que comme Zacharie exerçait la sacrificature devant le Seigneur, à son tour;
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 Selon la coutume d'exercer la sacrificature, le sort lui échut d'offrir le parfum et d'entrer [pour cet effet] dans le Temple du Seigneur.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Et toute la multitude du peuple était dehors en prières, à l'heure qu'on offrait le parfum.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Et l'Ange du Seigneur lui apparut, se tenant au côté droit de l'autel du parfum.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Et Zacharie fut troublé quand il le vit, et il fut saisi de crainte.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Mais l'Ange lui dit: Zacharie, ne crains point; car ta prière est exaucée, et Elisabeth ta femme enfantera un fils, et tu appelleras son nom Jean.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Et tu en auras une grande joie, et plusieurs se réjouiront de sa naissance.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Car il sera grand devant le Seigneur, et il ne boira ni vin ni cervoise; et il sera rempli du Saint-Esprit dès le ventre de sa mère.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Et il convertira plusieurs des enfants d'Israël au Seigneur leur Dieu.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Car il ira devant lui animé de l'esprit et de la vertu d'Elie, afin qu'il ramène les cœurs des pères dans les enfants, et les rebelles à la prudence des justes, pour préparer au Seigneur un peuple bien disposé.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Alors Zacharie dit à l'Ange: comment connaîtrai-je cela? car je suis vieux, et ma femme est fort âgée.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Et l'Ange répondant lui dit: Je suis Gabriel qui me tiens devant Dieu, et qui ai été envoyé pour te parler, et pour t'annoncer ces bonnes nouvelles.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Et voici, tu seras sans parler, et tu ne pourras point parler jusqu'au jour que ces choses arriveront; parce que tu n'as point cru à mes paroles qui s'accompliront en leur temps.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Or le peuple attendait Zacharie, et on s'étonnait de ce qu'il tardait tant dans le Temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Mais quand il fut sorti, il ne pouvait pas leur parler, et ils connurent qu'il avait vu quelque vision dans le Temple; Car il le leur donnait à entendre par des signes; et il demeura muet.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Et il arriva que quand les jours de son ministère furent achevés, il retourna en sa maison.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Et après ces jours-là, Elisabeth sa femme conçut, et elle se cacha l'espace de cinq mois, en disant:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Certes, le Seigneur en a agi avec moi ainsi aux jours qu'il m'a regardée pour ôter mon opprobre d'entre les hommes.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Or au sixième mois, l'Ange Gabriel fut envoyé de Dieu dans une ville de Galilée, appelée Nazareth;
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 Vers une Vierge fiancée à un homme nommé Joseph, qui était de la maison de David; et le nom de la Vierge était Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Et l'Ange étant entré dans le lieu où elle était, lui dit: je te salue, [ô toi qui es] reçue en grâce; le Seigneur est avec toi; tu es bénie entre les femmes.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Et quand elle l'eut vu, elle fut fort troublée à cause de ses paroles; et elle considérait en elle-même quelle était cette salutation.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Et l'Ange lui dit: Marie, ne crains point; car tu as trouvé grâce devant Dieu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Et voici, tu concevras en ton ventre, et tu enfanteras un fils, et tu appelleras son nom JESUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Il sera grand, et sera appelé le Fils du Souverain, et le Seigneur Dieu lui donnera le trône de David son père.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 Et il régnera sur la maison de Jacob éternellement, et il n'y aura point de fin à son règne. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Alors Marie dit à l'Ange: comment arrivera ceci, vu que je ne connais point d'homme?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Et l'Ange répondant lui dit: le Saint-Esprit surviendra en toi, et la vertu du Souverain t'enombrera; c'est pourquoi ce qui naîtra [de toi] Saint, sera appelé le Fils de Dieu.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Et voici, Elizabeth, ta cousine, a aussi conçu un fils en sa vieillesse; et c'est ici le sixième mois de la grossesse de celle qui était appelée stérile.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Car rien ne sera impossible à Dieu.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Et Marie dit: voici la servante du Seigneur; qu'il me soit fait selon ta parole! Et l'Ange se retira d'avec elle.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Or en ces jours-là Marie se leva, et s'en alla en hâte au pays des montagnes dans une ville de Juda.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Et elle entra dans la maison de Zacharie, et salua Elisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Et il arriva qu'aussitôt qu'Elisabeth eut entendu la salutation de Marie, le petit enfant tressaillit en son ventre, et Elisabeth fut remplie du Saint-Esprit.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 Et elle s'écria à haute voix, et dit: tu es bénie entre les femmes, et béni [est] le fruit de ton ventre.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Et d'où me vient ceci, que la mère de mon Seigneur vienne vers moi?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Car voici, dès que la voix de ta salutation est parvenue à mes oreilles, le petit enfant a tressailli de joie en mon ventre.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Or bienheureuse est celle qui a cru: car les choses qui lui ont été dites par le Seigneur, auront [leur] accomplissement.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Alors Marie dit: Mon âme magnifie le Seigneur;
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Et mon esprit s'est égayé en Dieu, qui est mon Sauveur.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Car il a regardé la bassesse de sa servante; voici, certes désormais tous les âges me diront bienheureuse.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Car le Puissant m'a fait de grandes choses, et son Nom est Saint.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Et sa miséricorde est de génération en génération en faveur de ceux qui le craignent.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Il a puissamment opéré par son bras; il a dissipé les desseins que les orgueilleux formaient dans leurs cœurs.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Il a renversé de dessus leurs trônes les puissants, et il a élevé les petits.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Il a rempli de biens ceux qui avaient faim; il a renvoyé les riches vides.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Il a pris en sa protection Israël, son serviteur, pour se souvenir de sa miséricorde;
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 ( Selon qu'il [en] a parlé à nos pères, [savoir] à Abraham et à sa postérité) à jamais. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Et Marie demeura avec elle environ trois mois, puis elle s'en retourna en sa maison.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Or le terme d'Elisabeth fut accompli pour accoucher; et elle mit au monde un fils.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Et ses voisins, et ses parents ayant appris que le Seigneur avait fait éclater sa miséricorde envers elle, s'en réjouissaient avec elle.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Et il arriva qu'au huitième jour ils vinrent pour circoncire le petit enfant, et ils l'appelaient Zacharie, du nom de son père.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Mais sa mère prit la parole, et dit: Non, mais il sera nommé Jean.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Et ils lui dirent: il n'y a personne en ta parenté qui soit appelé de ce nom.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Alors ils firent signe à son père, qu'il déclarât comment il voulait qu'il fût nommé.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Et [Zacharie] ayant demandé des tablettes, écrivit: Jean est son nom; et tous en furent étonnés.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Et à l'instant sa bouche fut ouverte, et sa langue [déliée], tellement qu'il parlait en louant Dieu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Et tous ses voisins en furent saisis de crainte; et toutes ces choses furent divulguées dans tout le pays des montagnes de Judée.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Et tous ceux qui les entendirent les mirent en leur cœur, disant: que sera-ce de ce petit enfant? et la main du Seigneur était avec lui.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Alors Zacharie son père fut rempli du Saint-Esprit, et il prophétisa, disant:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Béni soit le Seigneur, le Dieu d'Israël, de ce qu'il a visité et délivré son peuple;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Et de ce qu'il nous a suscité un puissant Sauveur dans la maison de David, son serviteur.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 Selon ce qu'il avait dit par la bouche de ses saints Prophètes, qui ont été de tout temps; (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 [Que] nous serions sauvés [de la main] de nos ennemis, et de la main de tous ceux qui nous haïssent;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Pour exercer sa miséricorde envers nos pères, et pour avoir mémoire de sa sainte alliance;
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 [Qui est] le serment qu'il a fait à Abraham notre père;
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 [Savoir], qu'il nous accorderait, qu'étant délivrés de la main de nos ennemis, nous le servirions sans crainte.
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 En sainteté et en justice devant lui, tous les jours de notre vie.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Et toi, petit enfant, tu seras appelé le Prophète du Souverain; car tu iras devant la face du Seigneur, pour préparer ses voies;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 Et pour donner la connaissance du salut à son peuple, dans la rémission de leurs péchés;
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Par les entrailles de la miséricorde de notre Dieu, desquelles l'Orient d'en haut nous a visités.
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 Afin de reluire à ceux qui sont assis dans les ténèbres et dans l'ombre de la mort, et pour conduire nos pas dans le chemin de la paix.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Et le petit enfant croissait, et se fortifiait en esprit; et il fut dans les déserts jusqu'au jour qu'il devait être manifesté à Israël.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luc 1 >